fidelitybank

Duk wanda zai koyar a makarantun sakandare sai ya na da digiri na biyu – Gwamnan Taraba

Date:

Gwamnan jihar Taraba, Dr Agbu Kefas, ya bayyana cewa digiri na biyu shi ne mafi karancin cancantar karatu ga duk wanda ke son koyarwa a makarantun sakandaren jihar.

Gwamnan ya bayyana shirye-shiryen da gwamnatinsa ta yi na fannin ilimi a lokacin wani liyafar cin abincin dare da manema labarai a Jalingo a ranar 7 ga watan Janairu.

A cewarsa, mafi karancin cancantar karatun malaman makarantun firamare shi ne matakin digiri na farko a jami’a, yana mai jaddada cewa nan ba da dadewa ba ne za a kammala takardar shedar karatu ta kasa NCE a matsayin mafi karanci ga malaman firamare.

Ya yi nuni da cewa, za a sake dawo da karatun Tarihi a matsayin darasi a cikin manhajar ilimi na farko tun daga makarantun firamare a jihar.

Kefas ya ce; “Za mu dawo da karatun Tarihi a makarantunmu na firamare da sakandare da ke jihar domin kafa ginshikin ci gaba cikin sauri.

“Ba da nisa ba, dole ne malaman firamare a jihar su zama masu digiri na farko yayin da malaman makarantun sakandare su sami mafi karancin digiri na biyu don inganta ilimin jihar.

“Wannan shi ne babban dalilin da ya sa muka rage kudin makaranta ga daliban da suka kammala digiri a jami’ar jihar. Dole ne mu tabbatar da kyakkyawar makoma ga yaranmu. Manufarmu ta ilimi kyauta ba abin wasa ba ne kuma duk wanda ya tsaya kan hanyar cimma hakan za a murkushe shi.”

Gwamnan ya yi kira ga ‘yan jarida da su sanya ido kan yadda gwamnatin jihar ke aiwatar da manufofin ilimi kyauta a makarantun firamare da sakandire domin tabbatar da cewa dukkan shugabannin makarantun suna yin abin da ya dace.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp