fidelitybank

Duk wanda yaki karbar tsohon kudi a Zamfara ku kama shi – Matawalle

Date:

Gwamnan jihar Zamfara, Muhammad Bello Matawalle, ya bayar da umarnin kama duk mutumin da ya ƙi karɓar tsofaffin takardun kuɗi a jihar.

A wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran gwamnan ya fitar, gwamnan ya ce za a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗin har zuwa lokacin da kotun ƙolin ƙasar za ta bayar da hukuncin ƙarshe game da ƙarar jihohin arewacin ƙasar uku suka kai gabanta suna ƙalubalantar matakin.

A makon da ya gabata ne dai jihohin Kaduna da Kogi da kuma zamfara suka kai Babban Bankin ƙasar da gwamnatin tarayya ƙara gaban kotun ƙolin ƙasar kan batun wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar.

Gwamna Matawalle ya bayar da umarnin ne a lokacin da yake rantsar da alƙalan babbar kotun jihar da sabbin masu ba shi shawara na musamman a Gusau fadar gwamnatin jihar..

Gwaman ya ce sun je kotun ƙolin ne shi da takwarorinsa gwamnonin jihohin Kaduna da Kogi, inda suka buƙaci kotun da ta bayar da umarnin ƙara wa’adin amfani da tsofafin takardun kuɗin.

Ya ƙara da cewa ”Wannan mataki da kotun ƙoli ta ɗauka ya taimaka wajen kare ƙasar nan daga faɗawa cikin rikice-rikice, waɗanda ka iya shafar zaman lafiya da kwanciyar hankalin ƙasar, lamarin da zai iya shafar babban zaɓen ƙasa da aka shirya gudanarwa cikin wannan wata”.

Gwamnan ya kuma bayyana farin cikinsa game da ci gaba da amfanin da tsofaffin takardun kuɗin ƙasar a harkokin kasuwanci da hada-hadar yau da kullum.

“Muna gode wa Allah kasancewar mutane za su ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗin a harkokin kasuwanci domin samun abun biyan buƙatunsu na yau da kullum ba tare da wata fargaba ba” in Matawalle.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...
X whatsapp