fidelitybank

Duk wanda yaki karbar tsohon kudi a Zamfara ku kama shi – Matawalle

Date:

Gwamnan jihar Zamfara, Muhammad Bello Matawalle, ya bayar da umarnin kama duk mutumin da ya ƙi karɓar tsofaffin takardun kuɗi a jihar.

A wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran gwamnan ya fitar, gwamnan ya ce za a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗin har zuwa lokacin da kotun ƙolin ƙasar za ta bayar da hukuncin ƙarshe game da ƙarar jihohin arewacin ƙasar uku suka kai gabanta suna ƙalubalantar matakin.

A makon da ya gabata ne dai jihohin Kaduna da Kogi da kuma zamfara suka kai Babban Bankin ƙasar da gwamnatin tarayya ƙara gaban kotun ƙolin ƙasar kan batun wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar.

Gwamna Matawalle ya bayar da umarnin ne a lokacin da yake rantsar da alƙalan babbar kotun jihar da sabbin masu ba shi shawara na musamman a Gusau fadar gwamnatin jihar..

Gwaman ya ce sun je kotun ƙolin ne shi da takwarorinsa gwamnonin jihohin Kaduna da Kogi, inda suka buƙaci kotun da ta bayar da umarnin ƙara wa’adin amfani da tsofafin takardun kuɗin.

Ya ƙara da cewa ”Wannan mataki da kotun ƙoli ta ɗauka ya taimaka wajen kare ƙasar nan daga faɗawa cikin rikice-rikice, waɗanda ka iya shafar zaman lafiya da kwanciyar hankalin ƙasar, lamarin da zai iya shafar babban zaɓen ƙasa da aka shirya gudanarwa cikin wannan wata”.

Gwamnan ya kuma bayyana farin cikinsa game da ci gaba da amfanin da tsofaffin takardun kuɗin ƙasar a harkokin kasuwanci da hada-hadar yau da kullum.

“Muna gode wa Allah kasancewar mutane za su ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗin a harkokin kasuwanci domin samun abun biyan buƙatunsu na yau da kullum ba tare da wata fargaba ba” in Matawalle.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp