fidelitybank

Duk wanda yaki karbar tsohon kudi a Jigawa ku kai kararsa – Badaru

Date:

Gwamnatin Jigawa ta ce, har yanzu tsofaffin takardun kuɗi na naira 500 da 1000 da Babban Bankin Najeriya ya ce sun daina aiki, kuma Shugaba Buhari ya jaddada hakan, suna aiki a jihar, har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci.

Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin matasa da wasanni da kuma al’adu, Ibrahim Mamsa, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa a jiya Alhamis.

Gwamnatin Jigawar ta bayyana wannan matsayi ne, da ke zaman bijire wa sanarwar da shugaban ƙasar, wanda a jawabin da ya yi jiya Alhamis ya ce naira 200 ce daga cikin takardun uku na 200 da 500 da 1000 za ta ci gaba da aiki, har zuwa ranar 10 ga watan Afirilu na wannan shekara.

Sanarwar ta ce gwamnati ta samu labarin cewa wasu mutane da kamfanoni (bankuna) ba sa karɓar takardun tsofaffin kuɗin a jihar kuma hakan ya dame ta.

Gwamnatin ta buƙaci jama’ar jihar da su kai rahoton duk wani ɗan kasuwa ko wani kamfani ko banki da suka ƙi karɓar tsofaffin takardun kuɗin na naira 200 da 500 da kuma ga hukumar da ta dace a jihar.

Gwamnatin Jigawa na cikin jihohi tara da suka bi sahun gwamnonin jihohin Kaduna da Zamfara da Kogi wajen kai ƙarar gwamnatin tarayya Kotun Koli kan batun canjin kuɗin da Babban Bankin ƙasar ya yi.

Shi ma gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya umarci jama’a a jiharsa su ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗin.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...
X whatsapp