fidelitybank

Duk wanda ya yi zanga-zanga ba da yawu na ba – Ajaka

Date:

Dan takarar gwamna na jam’iyyar SDP a zaben gwamnan jihar Kogi na ranar 11 ga watan Nuwamba, Muritala Yakubu Ajaka, a wa ya nisanta kansa daga wata zanga-zangar da magoya bayan jam’iyyarsa suka shirya yi a Lokoja da Abuja a lokaci guda a yau, Asabar.

A wani faifan bidiyo mai tsawon dakika 41 da ya fitar a daren Juma’a, Ajaka, wanda ke neman sakamakon zaben gwamnan jihar Kogi a kotu, ya bayyana cewa wadanda ke shirin gudanar da zanga-zangar a Lokoja da Abuja wakilan jam’iyyar APC mai mulki ne.

Dan takarar Gwamnan na SDP wanda ya fusata ya yi kira ga jami’an tsaro da su kame duk wani mai zanga-zanga da sunan sa ko jam’iyyar sa.

Kalamansa: “Yanzu an sanar da ni wani shirin zanga-zangar da wasu mutane ke da’awar cewa su ‘ya’yan jam’iyyar Social Democratic Party, SDP ne, ko kuma suna aiki da umarnina. Ban ba da izinin wata zanga-zanga a Lokoja ko Abuja gobe, (Asabar).

“Duk wanda ya yi zanga-zanga da sunana a kama shi. Dukkansu wakilan Gwamna Yahaya Bello ne masu kokarin haifar da rudani a jihar da kuma watakila a Abuja.

“Don haka don Allah ya kamata hukumomin tsaro su lura su kama wadannan mutane. Duk wanda aka gani da SDP vest gobe (Asabar) yana zanga-zanga, to a kama su. Wakilan Yahaya Bello ne”.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp