fidelitybank

Duk wanda ya samu nasara a zaben jihar Edo a ba shi – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi kira da dukkan masu ruwa da tsaki a jihar Edo da su tabbatar an martaba ƙuri’a da zaɓin mutanen Edo a zaɓen da za a yi gobe.

Tinubu ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a ta hannun mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga.

“Shugaba Tinubu yana kira ga ƴan takara da jam’iyyu da magoya baya da su martaba tsarin dimokuraɗiyya da zaɓin mutane. Ya yi ammanar cewa mutanen za su yi zaɓi wanda suka ga ya dace da shugabantarsu,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Da yake kira ga Hukumar INEC da jami’an tsaro su kasance na kowa, Shugaba Tinubu ya ce dole kowane ɓangare ya gudanar da harkokinsa cikin lumana.

Tinubu ya nanata cewa domokuraɗiyya na cigaba ne idan akwai fahimtar juna da hakuri da kuma girmama tsarin ƙasa, inda ya ƙara da cewa INEC ta ɗauki alwashin gudanar da zaɓe sahihi.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp