fidelitybank

Duk wanda ya nemi cin hanci kar ku ba shi – Tinubu

Date:

Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ya shaida wa masu zuba jari na ƙasar Qatar cewa, su kai masa rahoton duk wani jami’in Najeriya da ya nemi a ba shi cin hanci.

Tinubu ya bayyana hakan ne a wajen taron kasuwanci da zuba jari tsakanin ƴankasuwan Najeriyar da masu zuba jarin na Qatar, birnin Doha a ranar Lahadi.

Inda ya bayyana wa taron cewa gwamnatinsa a shirye ta ke ta ɗauki matakin da ya dace kan duk wanda ke neman kawo tsaiko ko kashe guiwar masu zuba jari a Najeriya.

“Na zo nan ne domin na baku tabbacin cewa muna yin garambawul. Duk wata matsala da wasunku suka fuskanta a baya, ya riga ya wuce, ba za ku gamu da irinta ba a nan gaba,” in ji Tinubu.

Inda ya ƙara da cewa “Kada ku bai wa kowa a cikin mutane na cin hanci, idan kuma har sun nema ko sun karɓa a hannunku, ku kawo ƙararsu wurina. za ku samu ganina.”

Tinubu ya kuma bayyana musu cewa kuɗadensu za su kasance cikin aminci, yana mai cewa gwamnatinsa ta ƙarfafa batun yaƙi da cin hanci da rashawa da yaƙi da rashin tsaro.

Ministan masana’antu da kasuwanci na Qatar, Sheikh Mohammed bin Hamad bin Qassim Al Abdullah Al Thani, ya bayyana cewa ƙasarsa na sa ran yin amfani da damar da Najeriyar ta bayar, inda Qatar ɗin za ta fi bai fifiko sun haɗa da zuba sabbin jari a shirye-shiryen da suka shafi rage iska mai gurɓata muhalli da ma’adanai, sinadaran da ake samu daga ɗanyen mai, fannin masana’antu da kuma abubuwan ci.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp