Shugaban Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Majalisar Dinkin Duniya, Tom Fletcher, ya mayar da martani game da mummunan labarin hare-haren da Isra’ila ke kaiwa Gaza.
Fletcher, a cikin wani sakon tweet a kan X ranar Talata, ya yi kira ga duk wanda ke da tasiri da ya dakatar da hare-haren.
“Ma’aikatan jin kai sun yi duk mai yiwuwa don ceton rayuka da yawa kamar yadda za mu iya a Gaza kuma yanzu wannan,” in ji Fletcher.
“Duk mai tasiri dole ne ya dage wannan tsayawa.”
Idan dai za a iya tunawa a baya sojojin Isra’ila sun bayyana cewa sun kai hari a yankunan Gaza da sanyin safiyar ranar Talata, lamarin da ya kawo karshen takun sakar da aka shafe makonni ana gwabzawa a tsakanin Isra’ila da kungiyar Hamas ta Falasdinu a watan Janairu.
Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu a Gaza daga baya ta ba da rahoton cewa a kalla mutane 326 ne suka mutu.
Ana sa ran adadin zai karu a cikin sa’o’i masu zuwa yayin da da yawa ke ci gaba da zama a karkashin baraguzan gine-ginen da aka harba.
A cewar ma’aikatar lafiya ta kasar, an sami rahotannin kai hare-hare a wurare da dama, da suka hada da arewacin Gaza, da birnin Gaza, da Deir al-Balah, Khan Younis, da Rafah dake tsakiya da kudancin zirin Gaza.