Kakakin mjalisar wakilai, Femi Gbajabiamila, ya gargadi masu rike da mukaman siyasa da ke da muradin yin takara a 2023, da su yi murabus daga mukaminsu.
A cewar Gbajabiamila, masu rike da mukaman siyasa na da hadari ga kansu da jamâiyyunsu idan suka ki yin murabus.
Sashi na 84(12) na dokar zabe ta 2022 wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya wa hannu kwanan nan ya ce, âBabu wani dan siyasa a kowane mataki da zai zama wakili mai kada kuriâa ko a zabe shi a babban taron ko taron wata jamâiyyar siyasa.â
Hakan na nufin masu rike da mukaman siyasa wadanda suke da buri, sai sun yi murabus kafin su fito takara.
Irin su Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, Ministan Shariâa kuma Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Malami, Karamin Ministan Ilimi, Chukwuemeka Nwajiuba da Ministan Kwadago da Aiki, Chris Ngige sun ki yin murabus duk da burinsu.
Gbajabiamila a wata hira da gidan talabijin na Channels TV ya ce, wasu masu rike da mukaman siyasa sun dage kan su yi murabus kafin su tsaya takara a zaben 2023 mai zuwa.
Shugaban majalisar yayin da yake magana kan matakin na su ya yi gargadin cewa, wanda aka nada a siyasa zai iya mayar da zaben fidda gwani na jamâiyyarsu a matsayin holoko.