fidelitybank

Duk wanda suka sace kayan abinci zai dandani kudar sa – Gwamnan Sokoto

Date:

Gwaman jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, ya gargaɗi waɗanda gwamnatin jihar ta bai wa aikin raba kayan aikin noman rani da su kauce wa ayyukan rashin gaskiya da “cin amanar da aka ba su”.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ƙaddamar da aikin raba kayan noman rani a garin Wamako na jihar ta Sokoto a ranar Litinin.

Ya ce “Ina gargaɗin ku da kakkausar murya, kada ku ci amanar da aka ba ku kamar yadda ya faru a lokacin damina.

“Mun ɗauki matakan tabbatar da cewa an hukunta duk wanda ya yi yunƙurin karkatar da kayan a wannan karo.

“Ku kasance masu tsoron Alla, ku bari al’umma su amfana da wannan tsari na gwamnati.”

Gwamna Aliyu ya ce gwamnatin Sokoto na ganin cewa babbar hanyar bunƙasa rayuwar al’ummar jihar ita ce ta hanyar bunƙasa ɓangaren noma.

Ya ce gwamnatinsa za ta raba filayen noman rani hekta 450 ga manoma a yankin Kware, sannan an fara aikin noman rani na Wurno yayin da aka bayar da kwangilar farfaɗo da madatsar ruwa ta Lugu Dam.

Noma ne babbar sana’ar al’ummar yankin arewacin Najeriya, sai dai a shekarun baya-bayan nan ɓangaren na noma ya samu koma-baya sanadiyyar matsalar tsaro.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp