Gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya ce, zai goyi bayan duk wanda ya zama dan takarar shugaban kasa a jamâiyyar PDP.
Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba bayan ziyarar ban girma da ya kai wa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Sanata Ahmed Makarfi.
Ko da shi kansa dan takarar shugaban kasa, Bala ya ce, dalilinsa na karbar duk wanda ya ci zaben fidda gwani shi ne ya tabbatar da cewa, PDP ta kwato shugaban kasa daga APC mara inganci.