Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Kano (KEDCO) ya bankado sama da gidaje 60,000 da suka kauracewa mitar wutar lantarkin su a cikin watanni shida da suka gabata.
A cewar hukumar, hakan ya jawo wa kamfanin asara mai dimbin yawa a cikin wannan lokaci.
A wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin na KEDCO, Ibrahim Sani Shawai ya fitar a ranar Talata, hukumar ta lura da cewa ta la’akari da tabarbarewar tattalin arzikin da wadannan gidaje suka haifar ne ya sa kamfanin ya kafa wata babbar runduna domin tsaftace tsarin.
Rundunar za ta tabbatar da aiki na duk mita da aka sanya tare da tabbatar da cewa gidaje suna sayarwa a lokaci da kuma lokacin domin guje wa satar makamashi.
A cewar shugaban Dr. Jamil Isyaku Gwamna, “Wannan wani babban zagon kasa ne ga wani kamfani da ya yi kokarin inganta wutar lantarki ga dimbin abokan huldar sa a fadin jihohin Kano da Katsina tare da Jigawa.”
Dr. Jamil Gwamna, ya bukaci kwastomominsu da su daina yin ta’ammali da mitoci, domin duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya kamar yadda dokar kasar ta tanada.