fidelitybank

Duk wanda muka kama ya na kauracewa Mita zamu gurfanar da shi – KEDCO

Date:

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Kano (KEDCO) ya bankado sama da gidaje 60,000 da suka kauracewa mitar wutar lantarkin su a cikin watanni shida da suka gabata.

A cewar hukumar, hakan ya jawo wa kamfanin asara mai dimbin yawa a cikin wannan lokaci.

A wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin na KEDCO, Ibrahim Sani Shawai ya fitar a ranar Talata, hukumar ta lura da cewa ta la’akari da tabarbarewar tattalin arzikin da wadannan gidaje suka haifar ne ya sa kamfanin ya kafa wata babbar runduna domin tsaftace tsarin.

Rundunar za ta tabbatar da aiki na duk mita da aka sanya tare da tabbatar da cewa gidaje suna sayarwa a lokaci da kuma lokacin domin guje wa satar makamashi.

A cewar shugaban Dr. Jamil Isyaku Gwamna, “Wannan wani babban zagon kasa ne ga wani kamfani da ya yi kokarin inganta wutar lantarki ga dimbin abokan huldar sa a fadin jihohin Kano da Katsina tare da Jigawa.”

Dr. Jamil Gwamna, ya bukaci kwastomominsu da su daina yin ta’ammali da mitoci, domin duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya kamar yadda dokar kasar ta tanada.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp