fidelitybank

Duk wanda muka kama ya na kauracewa Mita zamu gurfanar da shi – KEDCO

Date:

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Kano (KEDCO) ya bankado sama da gidaje 60,000 da suka kauracewa mitar wutar lantarkin su a cikin watanni shida da suka gabata.

A cewar hukumar, hakan ya jawo wa kamfanin asara mai dimbin yawa a cikin wannan lokaci.

A wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin na KEDCO, Ibrahim Sani Shawai ya fitar a ranar Talata, hukumar ta lura da cewa ta la’akari da tabarbarewar tattalin arzikin da wadannan gidaje suka haifar ne ya sa kamfanin ya kafa wata babbar runduna domin tsaftace tsarin.

Rundunar za ta tabbatar da aiki na duk mita da aka sanya tare da tabbatar da cewa gidaje suna sayarwa a lokaci da kuma lokacin domin guje wa satar makamashi.

A cewar shugaban Dr. Jamil Isyaku Gwamna, “Wannan wani babban zagon kasa ne ga wani kamfani da ya yi kokarin inganta wutar lantarki ga dimbin abokan huldar sa a fadin jihohin Kano da Katsina tare da Jigawa.”

Dr. Jamil Gwamna, ya bukaci kwastomominsu da su daina yin ta’ammali da mitoci, domin duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya kamar yadda dokar kasar ta tanada.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp