fidelitybank

Duk wanda muka kama ya na kauracewa Mita zamu gurfanar da shi – KEDCO

Date:

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Kano (KEDCO) ya bankado sama da gidaje 60,000 da suka kauracewa mitar wutar lantarkin su a cikin watanni shida da suka gabata.

A cewar hukumar, hakan ya jawo wa kamfanin asara mai dimbin yawa a cikin wannan lokaci.

A wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin na KEDCO, Ibrahim Sani Shawai ya fitar a ranar Talata, hukumar ta lura da cewa ta la’akari da tabarbarewar tattalin arzikin da wadannan gidaje suka haifar ne ya sa kamfanin ya kafa wata babbar runduna domin tsaftace tsarin.

Rundunar za ta tabbatar da aiki na duk mita da aka sanya tare da tabbatar da cewa gidaje suna sayarwa a lokaci da kuma lokacin domin guje wa satar makamashi.

A cewar shugaban Dr. Jamil Isyaku Gwamna, “Wannan wani babban zagon kasa ne ga wani kamfani da ya yi kokarin inganta wutar lantarki ga dimbin abokan huldar sa a fadin jihohin Kano da Katsina tare da Jigawa.”

Dr. Jamil Gwamna, ya bukaci kwastomominsu da su daina yin ta’ammali da mitoci, domin duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya kamar yadda dokar kasar ta tanada.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp