fidelitybank

Duk wanda bai yadda da kaddara ba imanin sa ragagge ne – Muhammadu II

Date:

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya ce babu wanda zai iya tuhumar Allah dangane da ƙaddara. Sabon sarkin ya faɗi hakan ne yayin huɗubar sallar Juma’a a masallacin sarki da ke Ƙofar Kudu a birnin Kano.

Huɗubar dai ta mayar da hankali ne kan imani da ƙaddara mai kyau ko marar kyau.

” Duk wanda ya yi imani da Allah shi kaɗai to dole ne ya yi imanin duk abin da Allah ya ƙaddara. Ba a tambayar ubangiji dalilin aiwatar da al’amura.

An faɗa mana cewa duk wanda bai yarda da ƙaddara ba cewa daga Allah take, imaninsa bai cika ba. Ya kamata mu zama masu godiya ga Allah a yanayi daɗi ko wuya. Dole ne mu yarda cewa duk abin da ya faru a gare mu ta ƙaddara ce daga Allah, sannan abin da ba mu iya samu ba shi ma daga Allah ne.” In ji Sarki Sanusi.

Daga ƙarshe sarkin ya ja hankalin masallatan da su mayar da hankali kan kwanaki 10 na watan Dhulhijja da ke ƙaratowa.

“Watan babbar sallah na ƙara tunkarowa wanda kuma yana da matuƙar muhimmanci, ya kamata mu mayar da hankali wajen addu’o’i a kwanakin.” In ji Sarki Sanusi.

Daga nan ne kuma Muhammadu Sanusi ya ja sallar ta Juma’a.

Da ma dai rundunar ‘yan sanda jihar Kano ta ƙaryata labaran da ke yawo a birnin cewa akwai yiwuwar yin arangama tsakanin Muhammadu Sanusi da Aminu Ado Bayero a masallacin.

Masu sarautar biyu dai sun kwashe mako guda kowa na iƙrarin kasancewa Sarkin Kano.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp