fidelitybank

Duk wadda ta haifi ƴan biyu ta na da kyautar dubu 50 – Matar Gwamnan Akwa Ibom

Date:

Matan da suka haifi tagwaye a Akwa Ibom za su rika samun tallafin kuɗi naira 50,000, yayin da za a bai wa matan da suka haifi ƴan uku kuma N10,000.

Mai ɗakin gwamnan jihar, Mrs Patience Umo Eno ce ta bayyana haka a lokacin wani taro karkashin shirin karfafawa mata masu haihuwa a jihar.

Da take bayyana batu bayar da tallafin kuɗin a mazaɓar Ikot Ekpene, Mrs Eno ta ce samar da kuɗaɗen alawus-alawus na wata-wata ga waɗanda za su ci gajiyar shirin, an yi shi ne don rage wa iyalai nauyin kula da ƴaƴansu musamman waɗanda ke haihuwa da yawa..

Mrs Eno ta faɗa wa iyaye a mazaɓar Eket da suka haihu da yawa cewa, “Kun ga nagarta da alherin Allah. Yana kyau ku yi murna da abin da Alla ya ba ku kuma shi ya sa muka taru a nan.

“Ina son tagwaye da ‘yan uku shi ya sa na sanya duk abin da zan iya a cikin wannan shiri. Ina so ku ƙara godiya ta hanyar nuna soyayya da kuma kula da yaran nan,” in ji mai ɗakin gwamnan.

Da yake jawabi, shugaban riko na karamar hukumar Ikot Ekpene, John Etim, ya yaba wa uwargidan gwamnan kan yadda ta rika tallafawa al’umma.

Ya ce hakan na taimakawa wajen bunƙasa gwamnatin jihar, inda ya kwatanta Mrs Eno a matsayin uwa mai tasiri a faɗin jihar.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa an raba wa matan da suka ci gajiya kayan jarirai da kuma kuɗi.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp