Alkali Peter Kekemeke na babbar kotun Abuja ya yanke wa korarrun ‘yan sanda 2 hukuncin kisa, bisa kama su da laifin fashi da makami.
Wadanda aka yanke wa hukuncin sun hada da James Ejah da Simeon Abraham wadanda kwamishinan ‘yan sandan Abuja ya gurfanar da su a shekarar 2017.
Yayin yanke hukuncin, Alkalin ya bayyana yadda aka kama su dumu-dumu da laifuka har shaidu hudu sai da suka tabbatar da laifukan su. Inji Daily Nigerian.
Yayin yanke hukuncin, Kekemeke ya bayyana yadda a ka kama korarrun ‘yan sandan dumu-dumu da laifukan, bayan shaidu hudu sun bayyana gaban kotu.
Alkalin ya shaida cewa, hujjojin da a ka gabatar gaban kotu sun nuna cewa, tabbas sun yi fashin. Ya kara da cewa babu wata shaida wacce ta zarce su da suka amsa laifukan su da bakunan su.