fidelitybank

Duk rintsi mu ne za mu samu nasara a jihar mu – Fubara

Date:

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya bayar da tabbacin cewa bayan duk rikice-rikicen da ake yi na siyasa a jihar, jihar ce za ta ci nasara.

Fubara ya bayyana haka ne a lokacin da ƙungiyoyin addini musulunci, ciki har da ƴan majalisar ƙoli ta addinin musulunci suka kai masa ziyarar gaisuwar sallah a gidansa da ke Fatakwal.

Da yake musu jawabi, Fubara ya ce su yi imani da abin da Allah ya tsara. “Yanzu lokaci ne na nuna ƙauna da sadaukar da kai. Kun zo ne domin nuna mana ƙauna. Na yi imanin cewa duk abin da ya faru Allah ne ya tsara, kuma ina da tabbacin nasara za ta biyo baya,” in ji shi kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

“Duk abin da ke faruwa, ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba domin mun yarda da ikon Allah. Na yi imanin cewa mu ne za mu samu nasara. Ko da kuwa akwai zafi da damuwa, ba matsala, abu mafi muhimmanci shi ne tsayawa kan gaskiya.”

A nasa jawabin tun farko, Alhaji Nasir Awhelebe Uhor ya ce sun je ne domin nuna goyon bayansu ga gwamnan, inda ya ce suna tare da shi, kuma suna masa addu’a domin samun nasara.

Ya yi kira ga gwamnan da ya haƙuri, inda ya ce masa Allah yana taimakon masu haƙuri.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp