Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya bayar da tabbacin cewa bayan duk rikice-rikicen da ake yi na siyasa a jihar, jihar ce za ta ci nasara.
Fubara ya bayyana haka ne a lokacin da ƙungiyoyin addini musulunci, ciki har da ƴan majalisar ƙoli ta addinin musulunci suka kai masa ziyarar gaisuwar sallah a gidansa da ke Fatakwal.
Da yake musu jawabi, Fubara ya ce su yi imani da abin da Allah ya tsara. “Yanzu lokaci ne na nuna ƙauna da sadaukar da kai. Kun zo ne domin nuna mana ƙauna. Na yi imanin cewa duk abin da ya faru Allah ne ya tsara, kuma ina da tabbacin nasara za ta biyo baya,” in ji shi kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.
“Duk abin da ke faruwa, ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba domin mun yarda da ikon Allah. Na yi imanin cewa mu ne za mu samu nasara. Ko da kuwa akwai zafi da damuwa, ba matsala, abu mafi muhimmanci shi ne tsayawa kan gaskiya.”
A nasa jawabin tun farko, Alhaji Nasir Awhelebe Uhor ya ce sun je ne domin nuna goyon bayansu ga gwamnan, inda ya ce suna tare da shi, kuma suna masa addu’a domin samun nasara.
Ya yi kira ga gwamnan da ya haƙuri, inda ya ce masa Allah yana taimakon masu haƙuri.