fidelitybank

Duk rintsi mu ne za mu samu nasara a jihar mu – Fubara

Date:

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya bayar da tabbacin cewa bayan duk rikice-rikicen da ake yi na siyasa a jihar, jihar ce za ta ci nasara.

Fubara ya bayyana haka ne a lokacin da ƙungiyoyin addini musulunci, ciki har da ƴan majalisar ƙoli ta addinin musulunci suka kai masa ziyarar gaisuwar sallah a gidansa da ke Fatakwal.

Da yake musu jawabi, Fubara ya ce su yi imani da abin da Allah ya tsara. “Yanzu lokaci ne na nuna ƙauna da sadaukar da kai. Kun zo ne domin nuna mana ƙauna. Na yi imanin cewa duk abin da ya faru Allah ne ya tsara, kuma ina da tabbacin nasara za ta biyo baya,” in ji shi kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

“Duk abin da ke faruwa, ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba domin mun yarda da ikon Allah. Na yi imanin cewa mu ne za mu samu nasara. Ko da kuwa akwai zafi da damuwa, ba matsala, abu mafi muhimmanci shi ne tsayawa kan gaskiya.”

A nasa jawabin tun farko, Alhaji Nasir Awhelebe Uhor ya ce sun je ne domin nuna goyon bayansu ga gwamnan, inda ya ce suna tare da shi, kuma suna masa addu’a domin samun nasara.

Ya yi kira ga gwamnan da ya haƙuri, inda ya ce masa Allah yana taimakon masu haƙuri.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp