Masu ruwa da tsaki a siyasar yankin Abia ta Arewa, sun bukaci ‘yan takarar sanata daga shiyyar da su janye aniyarsu ta nemawa Sanata Orji Uzor Kalu, inda suka bayyana cewa a shirye suke su dawo da kudaden sauran ‘yan takarar.
Kungiyar ta hada da sarakunan gargajiya, kungiyoyin matasa, kwararru a jihar Abia, malamai, fitattun ‘yan siyasa, da manyan ‘yan kasuwa, a karkashin kungiyar masu ruwa da tsaki ta Abia ta Arewa.
A wata sanarwa da kungiyar ta fitar a ranar Laraba, wadda aka rabawa jaridar The PUNCH, kungiyar ta yi kaca-kaca da zaben Kalu wanda shi ne bulalaiyar majalisar dattawa.
Shugaban kungiyar, Dakta Kalu Ncheghe, ya bayyana cewa, alkalumma sun nuna cewa bulaliyar majalisar Dattawan ya taka rawar gani, inda ya kara da cewa “Kungiyar ta yi imanin cewa ayyukan Kalu a matsayinsa na dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Abia ta Arewa shi ne mafi kyawu a tarihin jihar Abia, Najeriya gaba daya.”