fidelitybank

Duk mai Babur sai ya yi rijista ko a kama shi – FRSC

Date:

Shugaban hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa FRSC, Dauda Biu, ya umarci kwamandojin sassan kasa 37 da su kama duk wani babur ba tare da rajistar da ya dace ba.

Biu ya ba da umarnin ne a wata sanarwa da jami’in kula da ilimin jama’a na Corps Mista Bisi Kazeem ya fitar a Abuja ranar Litinin.

“Dukkan baburan da ba su da rajista za a kama su. Ana bukatar masu baburan su kammala cikakken rajistar baburan kafin a sako su.

“Duk babura da aka kama, dole ne a rubuta cikakkun bayanai,’’ in ji shi.

Shugaban na FRSC ya ce, umarnin ya zama dole ne, biyo bayan karuwar yawan babura da ke bin hanyoyin.

A cewarsa, akwai kuma bukatar a kama duk babura yadda ya kamata a cikin kundin tsarin tantance ababen hawa na kasa.

Ya yi nuni da cewa, umarnin zai taimaka wajen dakile rashin tsaro idan duk baburan da aka kama suna cikin ma’adanar bayanai ta kasa.

Biu ya bukaci kwamandojin sassan da su gaggauta tuntubar hukumomin tattara kudaden shiga na jihohinsu, domin kafa kwamitin da zai magance lamarin.

Ya kuma ba da umarnin cewa, a yi hadin gwiwa da jami’an ‘yan sanda da ofishin binciken ababan hawa da sauran masu ruwa da tsaki, domin tabbatar da aiwatar da aikin.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp