fidelitybank

Duk ma’aikacin da yake da shaidar karatu na bogi a kore shi daga aiki – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Tarayya ta bayar da amince a kori duk ma’aikata na gwamnati da waɗanda ba na gwamnati ba, waɗanda suke da takardar shedar karatu ta bogi, da suka samu daga Jamhuriyar Benin da Togo,

Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman shi ne ya bayyana haka a, yayin wani taron manema labarai, jiya Juma’a a Abuja, lokacin da yake bayyana irin nasarorin da ya ce ya samu a tsawon shekara ɗaya a ma’aikata.

Mamman ya ce an amince da matakin ne a lokacin taron majalisar zartarwa ta ƙasar kwanan nan.

Ministan ya bayyana cewa ƴan ƙasar sama da 22,500 ne ke ɗauke da takardar shedar karatu ta bogi da suka samu daga ƙasashe irin su, Jamhuriyar Benin da Togo, a tsakanin 2019 da 2023.

Ya ce sama da ɗalibai 21, 600, suka samu takardun shedar karatun daga jami’o’in da ba a tabbatar da ingancinsu ba a Jamhuriyar Benin yayin da 1,105 su ma suka samu irin waɗannan takardu daga jami’o’in da ba a tabbatar da ingancin nasu ba a Togo.

Ya ƙara da cewa a don haka ne gwamnati ta kafa wani kwamiti na musamman na haɗin gwiwa tsakanin ma’aikatu domin gudanar da bincike kan takardun shedae karatun, cibiyoyin da ke wannan cuwa-cuwa a ciki da wajen Najeriya.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp