Kungiyar shugabannin yankin Kudanci da kuma tsakiyar Najeriya ta gudanar da wani taro a Abuja na sake neman a mayar da mulki Kudu a kakar zaɓen 2023.
A cikin sanarwar da ta fitar a karshen taron na ranar Alhamis wanda ya samu halartar tsofaffin gwamnoni da ministoci da ƴan majalisun tarayya da na jihohi da manyan ƴan siyasa da kwararru daga shiyyar Kudu da tsakiyar Najeriyar.
BBC ta rawaito cewa, kungiyar ta yi kira ga dukkanin jam’iyyun siyasa, su kai tikitin takarar shugaban kasa zuwa Kudu.
Ta kuma yi gargaɗin cewa, duk wata jam’iyya da ta gaza yin hakan kada ta yi tsammanin samun goyon bayan shiyyoyin idan zaɓe ya zo.
“Tun da ɗan Arewa ne ya yi mulki na tsawon shekara 8 to lallai ya kamata shugabanci ya koma Kudu, duk wata jam’iyya da ta ƙi yin haka kuwa za ta gani a kwaryar shanta’’ inji wannan sanarwa.