fidelitybank

Duk inda aka ga Netanyahu a kama shi – ICC

Date:

Alƙalan kotun hukunta manyan laifuka wato ICC sun bayar da sammacin kama firaministan Isra’ila da tsohon ministan tsaron ƙasar da wasu kwamandojin Hamas.

Kotun ta yi watsi da yunƙurin Isra’ila na ƙalubalantar huruminta, inda bayan sauraron ƙara, ta bayar da sammacin kama Netanyahun da Yoav Gallant.

Haka kuma an bayar da sammacin kama Mohammed Deif, duk da cewa sojojin Isra’ila sun ce sun kashe shi a wani hari a Gaza a watan Yuli.

Alƙalan sun ce sun gamsu da hujjojin cewa mutanen uku sun “aikata laifukan yaƙi” da wasu laifukan cin zarafin mutane a yaƙin Isra’ila da Hamas. Sai dai Isra’ila da Hamas ɗin duk su musanta aikata laifukan yaƙi.

Yanzu hankali ya koma kan ƙasashe mambobin kotun duniyar guda 124 domin yanke shawarar tabbatar da umarnin kotun ko su yi watsi da shi.

A watan Mayu ne mai gabatar da ƙara na kotun hukunta manyan laifuka, Karim Khan ya buƙaci kotun ta bayar da sammacin kama Netanyahu da Gallant da Deif da wasu kwamandojin Hamas biyu, waɗanda an riga an kashe su wato Ismail Haniyeh da Yahya Sinwar. Duk da cewa Isra’ila ta ce ta kashe Deif, kotun ta ce ba ta tabbatar da hakan ba.

Mai gabatar da ƙarar ya shigar da ƙarar ce saboda abin da ya biyo bayan harin Hamas na 7 ga Oktoban 2023, wanda ya yi sanadiyar kashe kusan mutum 1,200 a arewacin Gaza, sannan suka yi garkuwa da mutum 251.

Isra’ila ta ƙaddamar da mayar da martani, inda ta kashe aƙalla mutum 44,000 a Gaza, kamar yadda ma’aikatar lafiya ta yankin wanda ke ƙarƙashin Hamas ta bayyana.

An zargi jagororin Hamas da kisa da garkuwa da mutane da fyaɗe da azabtarwa.

A gefe guda kuma an zargi Isra’ila da kai hare-hare kan fararen hula da gangan da amfani yunwa a matsayin makamin yaƙi da kashe-kashe

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp