fidelitybank

Duk inda aka ga Netanyahu a kama shi – ICC

Date:

Alƙalan kotun hukunta manyan laifuka wato ICC sun bayar da sammacin kama firaministan Isra’ila da tsohon ministan tsaron ƙasar da wasu kwamandojin Hamas.

Kotun ta yi watsi da yunƙurin Isra’ila na ƙalubalantar huruminta, inda bayan sauraron ƙara, ta bayar da sammacin kama Netanyahun da Yoav Gallant.

Haka kuma an bayar da sammacin kama Mohammed Deif, duk da cewa sojojin Isra’ila sun ce sun kashe shi a wani hari a Gaza a watan Yuli.

Alƙalan sun ce sun gamsu da hujjojin cewa mutanen uku sun “aikata laifukan yaƙi” da wasu laifukan cin zarafin mutane a yaƙin Isra’ila da Hamas. Sai dai Isra’ila da Hamas ɗin duk su musanta aikata laifukan yaƙi.

Yanzu hankali ya koma kan ƙasashe mambobin kotun duniyar guda 124 domin yanke shawarar tabbatar da umarnin kotun ko su yi watsi da shi.

A watan Mayu ne mai gabatar da ƙara na kotun hukunta manyan laifuka, Karim Khan ya buƙaci kotun ta bayar da sammacin kama Netanyahu da Gallant da Deif da wasu kwamandojin Hamas biyu, waɗanda an riga an kashe su wato Ismail Haniyeh da Yahya Sinwar. Duk da cewa Isra’ila ta ce ta kashe Deif, kotun ta ce ba ta tabbatar da hakan ba.

Mai gabatar da ƙarar ya shigar da ƙarar ce saboda abin da ya biyo bayan harin Hamas na 7 ga Oktoban 2023, wanda ya yi sanadiyar kashe kusan mutum 1,200 a arewacin Gaza, sannan suka yi garkuwa da mutum 251.

Isra’ila ta ƙaddamar da mayar da martani, inda ta kashe aƙalla mutum 44,000 a Gaza, kamar yadda ma’aikatar lafiya ta yankin wanda ke ƙarƙashin Hamas ta bayyana.

An zargi jagororin Hamas da kisa da garkuwa da mutane da fyaɗe da azabtarwa.

A gefe guda kuma an zargi Isra’ila da kai hare-hare kan fararen hula da gangan da amfani yunwa a matsayin makamin yaƙi da kashe-kashe

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp