Firai ministan Birtaniya, ya yi kira ga ƴan ƙasar mazauna Lebanon su gaggauta ficewa daga ƙasar a daidai lokacin da faɗa tsakanin Hezbollah da Isra’ila ke ƙara ƙazancewa.
Sir Keir Starmer ya ce “muna duba shirin da ya kamata mu yi, amma ina ganin ya kamata ku fice daga ƙasar, saboda akwai haɗarin barkewar yaƙi”.
Ma’aikatar tsaron Birtaniya za ta girke dakaru 700 a Cyprus, domin shirin ko ta kwana na kwashe ƴan ƙasar daga Lebanon, sannan a gargaɗi matafiya su kaucewa zuwa ƙasar.
Kawo yanzu sojin Isra’ila sun hallaka sama da mutum 500 tun bayan ƙaddamar da hari a Lebanon ranar Litinin, ciki har da mata da ƙananan yara 150.