fidelitybank

Duk da yunƙurin komawa PDP Tinubu zai gana da Shekarau

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, Bola Tinubu, ya gayyaci dan majalisa mai wakiltar mazabar Kano ta tsakiya, Ibrahim Shekarau, zuwa wani taron sirri a Abuja.

Ana sa ran Tinubu zai gana da tsohon gwamnan jihar Kano a babban birnin tarayya ranar Laraba.

Wata majiya da ta zanta da DailyNigerian ta bayyana cewa, Tinubu na shirin zawarcin Shekarau cikin jam’iyyar yayin ganawar.

Hakan na zuwa ne bayan rahotanni sun bayyana cewa, Shekarau ya cimma yarjejeniya da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya koma jam’iyyar.

Wata majiya da ta yi magana kan shirin Tinubu na neman Shekarau zuwa APC ta ce, tun da farko dan takarar shugaban kasa ya gana da Shekarau a ranar 8 ga watan Agusta, amma ba a cimma matsaya ba.

Majiyar ta ci gaba da cewa, duk da cewa Shekarau ya amince ya koma PDP, amma tsohon gwamnan ya gayyaci majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa, wato Shura Consultative Assembly, don ba shi shawara kan ci gaban.

Ana sa ran majalisar za ta gabatar da rahoto a yau kuma za a sanar da hukuncin a cikin mako guda

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp