fidelitybank

Duk da yunƙurin komawa PDP Tinubu zai gana da Shekarau

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, Bola Tinubu, ya gayyaci dan majalisa mai wakiltar mazabar Kano ta tsakiya, Ibrahim Shekarau, zuwa wani taron sirri a Abuja.

Ana sa ran Tinubu zai gana da tsohon gwamnan jihar Kano a babban birnin tarayya ranar Laraba.

Wata majiya da ta zanta da DailyNigerian ta bayyana cewa, Tinubu na shirin zawarcin Shekarau cikin jam’iyyar yayin ganawar.

Hakan na zuwa ne bayan rahotanni sun bayyana cewa, Shekarau ya cimma yarjejeniya da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya koma jam’iyyar.

Wata majiya da ta yi magana kan shirin Tinubu na neman Shekarau zuwa APC ta ce, tun da farko dan takarar shugaban kasa ya gana da Shekarau a ranar 8 ga watan Agusta, amma ba a cimma matsaya ba.

Majiyar ta ci gaba da cewa, duk da cewa Shekarau ya amince ya koma PDP, amma tsohon gwamnan ya gayyaci majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa, wato Shura Consultative Assembly, don ba shi shawara kan ci gaban.

Ana sa ran majalisar za ta gabatar da rahoto a yau kuma za a sanar da hukuncin a cikin mako guda

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp