Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta fitar da rahoton saukar hauhawar farashin kayan abinci a Najeriya, jihohi goma tare da babban birnin Tarayya, Abuja na ci gaba da fama da hauhawar farashi da ya haura kashi 30 cikin 100.
Wannan na nuna alamar cewa matsin tattalin arziki na ci gaba da gallaza wa al’umma a wasu sassan ƙasar.
Rahoton hauhawar farashi na wata-wata ya nuna cewa a watan Afrilun 2025 hauhawar farashi ya sauka zuwa kashi 23.71 cikin 100 idan aka kwatanta da kashi 24.23 cikin 100 a watan Maris da kuma kashi 33.69 cikin 100 a watan Afrilu na bara.
Sai dai duk da saukar farashin a matakin ƙasa, jihohin Enugu da Kebbi da Neja da Benue da Ekiti da Nassarawa da Zamfara da Delta da Gombe da Sokoto da kuma Abuja har yanzu suna fuskantar hauhawar farashi kayayyaki.
Jihar da ta fi fuskantar hauhawar farashi mafi muni ita ce Enugu inda ya kai kashi 36.0 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.
Na Kebbi da Niger ya kai kashi 35.1 da 34.8 cikin 100 bi da bi.
Farashin abinci na ci gaba da ƙara tsananta rayuwar jama’a a waɗannan jihohi.
A Jihar Benue, hauhawar farashin abinci ya kai kashi 51.8 cikin 100 idan aka kwatanta da bara, tare da ƙarin kashi 25.6 cikin 100 a cikin wata guda.
Wannan na da nasaba da rashin tsaro da ke kawo cikas ga noman abinci in ji rahoton.