fidelitybank

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Date:

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta fitar da rahoton saukar hauhawar farashin kayan abinci a Najeriya, jihohi goma tare da babban birnin Tarayya, Abuja na ci gaba da fama da hauhawar farashi da ya haura kashi 30 cikin 100.

Wannan na nuna alamar cewa matsin tattalin arziki na ci gaba da gallaza wa al’umma a wasu sassan ƙasar.

Rahoton hauhawar farashi na wata-wata ya nuna cewa a watan Afrilun 2025 hauhawar farashi ya sauka zuwa kashi 23.71 cikin 100 idan aka kwatanta da kashi 24.23 cikin 100 a watan Maris da kuma kashi 33.69 cikin 100 a watan Afrilu na bara.

Sai dai duk da saukar farashin a matakin ƙasa, jihohin Enugu da Kebbi da Neja da Benue da Ekiti da Nassarawa da Zamfara da Delta da Gombe da Sokoto da kuma Abuja har yanzu suna fuskantar hauhawar farashi kayayyaki.

Jihar da ta fi fuskantar hauhawar farashi mafi muni ita ce Enugu inda ya kai kashi 36.0 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

Na Kebbi da Niger ya kai kashi 35.1 da 34.8 cikin 100 bi da bi.

Farashin abinci na ci gaba da ƙara tsananta rayuwar jama’a a waɗannan jihohi.

A Jihar Benue, hauhawar farashin abinci ya kai kashi 51.8 cikin 100 idan aka kwatanta da bara, tare da ƙarin kashi 25.6 cikin 100 a cikin wata guda.

Wannan na da nasaba da rashin tsaro da ke kawo cikas ga noman abinci in ji rahoton.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp