fidelitybank

Duk da mirza gashin bakin ECOWAS Nijar ta naɗa sababbin Ministoci

Date:

Shugabannin mulkin soji a Nijar, sun sanar da naɗa ministoci.

Sojojin sun sanar da haka ne a wata doka da aka karanta a gidan talabijin na ƙasar a cikin dare.

Firaminista Ali Mahaman Lamine Zeine shi zai jagoranci mambobi 21 na gwamnatin, inda sabbin janar-janar ɗin gwamnatin mulkin sojin za su shugabanci ɓangaren tsaro da kuma harkokin cikin gida. In ji BBC.

Hakan na zuwa ne yayin da ECOWAS ke gudanar da taro yau Alhamis a Abuja domin yiwuwar ɗaukar matakin soja ko bin hanyar diflomasiyya wajen warware rikicin na Nijar.

Tun da farko sojojin na Nijar sun yi watsi da wa’adin da ECOWAS ta ba su na mayar da shugaba Mohamed Bazoum kan mulki.

Ga cikakken jerin sunayen mambobin majalisar zartarwar gwamnatin mulkin sojin Nijar, kamar yadda Mahamane Roufai Loauali, sakatare-najar na majalisar ya sanar

1. Firaminista kuma ministan kuɗi da tattalin arziki – Lamine Zeine Ali Mahamane

2. Ƙaramin ministan tsaron ƙasa – Laftanar-Janar Salifou Mody

3. Ƙaramin ministan harkokin cikin gida da tsaron al’umma – Birgediya-Janar Mohamed Toumba

4. Ministan matasa da wasanni – Kanar-Manjo Abdourahamane Amadou

5. Ministan harkokin ƙasashen waje da haɗa kan jama’ar Nijar da ke zama a waje – Bakary Yaou Sangare

6. Ministan lafiya da walwalar jama’a – Dr Kanar-Manjo Garba Hakimi

7. Ministan kula da majalisar ƙasa da tabbatar da lafiyar cikin gida – Dr Soumana Boubacar

8. Ministan noma da kiwo – Mahaman Elhadj Ousmane

9. Ministan ilimi mai zurfi da binciken kimiyya da fasaha – Farfesa Mahamadou Saidou

10. Ministar ilimi da koyar da sana’oin hannu da kuma bunƙasa harsunan ƙasa – Elizabeth Cherif

11. Ministan sufuri – Kanar Salissou Mahaman Salissou

12. Ministan muhalli da tsaftace ƙasa – Kanar Maizama Abdoulaye

13. Ministan shari’a da kare yancin dan-adam – Alio Daouda

14. Ministar ƙwadago da samar da ayyukan yi – Aissatou Abdoulaye Tondi

15. Ministan tsare-tsaren ƙasa da samar da gidaje – Salissou Sahirou Adamou

16. Ministan jin ƙai da agajin gaggawa – Aissa Lawan Wandarama.

17. Ministan man fetir da ma’adinai da kuma makamashi – Mahaman Moustapha Barke

18. Ministan yawon buɗe ido da sana’oi – Guichen Agaichata Atta

19. Ministan sadarwa da bunƙasa fasahar zamani – Sidi Mohamed Raliou

20. Ministan kasuwanci da masana’antu – Seydou Asman

21. Ministan harkokin kuɗi a ofishin firaminista – Moumouni Boubacar Saidou

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp