Dawan wasan gaba na Super Eagles, Moses Simon, ya ce suna sane da yadda Kamaru ke amfani da karfin tuwo wajen buga wasa, yayin da za su tunkare su.
A gobe Asabar ne tawagar Super Eagles ta Najeriya za ta gwabza da ta Indomitable Lions ta Kamaru a wasan zagaye na siri daya kwale na gasar Kofin Afirka ta 2023 da ke gudana a Ivory Coast.
Ya ce sun san cewa suna saka karfi sosai, amma su na da karfin tunkarar Kamaru.
Sai dai ya kuma ce karfin jiki ba shi ke kawo nasara ba, su burin su shi ne kawai su cinye su duk da ta hanyar da ta dace.
Wasa tsakanin kasashen biyu mai cike da tarihi, kuma karo na karshe da suka kara shi ne a 2019, inda Najeriya ta yi nasara da ci 3-2 a irin wannan zagayen na gasar.