fidelitybank

Duk da kararraki a kotu ba zai hana mu miƙawa Tinubu mulki ba – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa ƴan Najeriya cewa, duk da kalubalantar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da wasu jam’iyyu ke yi ba zai hana ta miƙa wa zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Bola Tinubu mulki ba.

Da yake magana da manema labarai a ranar Talata, shugaban kwamitin kuma sakataren gwamnatin tarayya, Boss Gida Mustapha, ya ce sun shirya tsaf domin miƙa mulki a ranar 29 ga watan Mayu cikin tsanaki ba tare da wata matsala ba.

Mustapha ya ce, ƙarar da wasu jam’iyyu suka shigar kan zaɓaɓɓen shugaban ƙasar da jam’iyyar APC da kuma INEC ba zai dakatar da shirye-shiryen da suke yi ba.

Ya ce tuni shirye-shiryen kwamitin ya yi nisa, inda ya ce an ɗora wa ƙaramin kwamitin tsaro na miƙa mulkin da ya tabbatar da cewa babu wani mahaluki da zai kawo tarnaki ga shirin miƙa mulkin.

A ranar 9 ga watan Febrairun 2023 ne shugaba Muhammadu Buhari ya amince da naɗin kwamitin wanda aka ɗora wa alhakin gudanar da dukkan ayyukan shirin miƙa mulki ga sabuwar gwamnati mai zuwa.

Mambobin kwamitin sun haɗa da sakataren gwamnatin tarayya wanda shi ne shugaban kwamitin da shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya.

Sauran sun haɗa da babban lauyan gwamnatin tarayya da babban sakatare a ma’aikatar shari’a da kuma manyan sakatarori daga waɗannan ma’aikatu na gwamnatin tarayya.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp