fidelitybank

Duk da an yi mana magudi a zaben Laberiya amma mun hakura – Jam’iyyar Adawa

Date:

Jam’iyyar shugaban ƙasar Laberiya George Weah, Coalition for Democratic Change (CDC), ta yi zargin cewa jam’iyyar adawa ta tafka maguɗi a zaɓen shugaban ƙasa zagaye na biyu da aka gudanar a makon da ya gabata.

Sai dai, jam’iyyar ta ce duk da cewa ta fito da batun, amma ba za ta kai batun gaba ba saboda tana son ganin haɗin-kai ya ci gaba da wanzuwa a Laberiya.

Shugaba Weah ya amsa shan kaye a ranar Juma’a da ta gabata lokacin da sakamako ya nuna cewa abokin takararsa, Joseph Boakai, yana kan gaba da karamar tazara.

Sakamakon karshe na zaɓen da aka fitar a ranar Litinin, ya nuna cewa Boakai ya samu nasara da kuri’u sama da 20,000.

Ƙungiyoyin sa ido kan zaɓe a ciki da wajen ƙasar, ciki har da ƙungiyar Ecowas da Tarayyar Turai, dukkansu sun ce zaɓukan sun gudana lami lafiya kuma cikin gaskiya.

Sai dai wani taron manema labarai da babban-sakataren jam’iyyar CDC Jefferson Koijee ya kira a ranar Laraba, ya ce jam’iyyarsa tana da hujjoji da ke nuna cewa ɓangaren adawa ya tafka maguɗi.

“Muna da kwararan hujjojin cewa an tafka maguɗi a zaɓen,” in ji shi.

Jam’iyyar Unity ta mista Boakai ba ta mayar da martani kan zarge-zargen ba.

A wani jawabinsa da ya watsu ko’ina a makon da ya gabata, mista Weah ya ce “Al’ummar Laberiya sun yi kira kuma mun amsa kiransu” kuma lokaci ne na amsa shan kaye, lokaci kuma na sanya buƙatar ƙasarmu a farko.

Sai dai ya ƙara da cewa CDC za ta ci gaba da zama babbar jam’iyyar adawa. Zai sauka daga kan mulki ne a watan Janairu.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp