Dubban jama’a a jihar Adamawa sun sauya sheka daga jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) zuwa jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP).
Wasu daga cikin tsoffin ‘yan jam’iyyar NNPP da suka fafata a wasu titunan birnin Yola a ranar Juma’a, an gansu sanye da hular kwakwasiyya, wanda shugaban NNPP na kasa, Rabi’u Kwankwaso ya yi farin jini.
Sai dai sun yi ta rera taken PDP tare da bayyana goyon bayansu ga dan takarar shugaban kasa na PDP Atiku Abubakar da dan takarar gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri.
Jagoran taron wanda tsohon sakataren jam’iyyar NNPP na shiyyar Arewa maso Gabas, Dr Babayo Liman ya ce sun fice daga NNPP ne saboda jam’iyyar na fama da rikici a jihohi da dama kuma shugaban na kasa wanda kuma ke neman zama shugaban kasa ya kasa magance su.
Babayo wanda dan jihar Bauchi ne, ya sanar da sauya sheka a farkon makon nan, inda ya ce magoya bayansa a Adamawa ne suka gayyace shi ya jagorance su zuwa PDP.
“Na sha samun gayyata daga jihohi daban-daban kuma da na zo nan (Adamawa), sai suka ce min suna son bin sawu na,” in ji shi, inda ya bayyana cewa akalla mutane 400,000 ne ke barin jam’iyyar NNPP zuwa PDP a jihar Adamawa.
Ya gabatar da wadanda suka biyo shi taron manema labarai da ya gudana a cibiyar ‘yan jarida ta NUJ da ke Yola, a matsayinsa na tsoffin jami’an NNPP na kananan hukumomin jihar Adamawa 21.
A yayin ganawar tasu da manema labarai, tsoffin ‘yan jam’iyyar NNPP sun cire kwankwasiyyarsu domin nuna alamar ficewarsu daga jam’iyyar NNPP.