fidelitybank

Dubban ‘yan NNPP sun juyawa jam’iyyar baya a Adamawa

Date:

Dubban jama’a a jihar Adamawa sun sauya sheka daga jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) zuwa jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP).

Wasu daga cikin tsoffin ‘yan jam’iyyar NNPP da suka fafata a wasu titunan birnin Yola a ranar Juma’a, an gansu sanye da hular kwakwasiyya, wanda shugaban NNPP na kasa, Rabi’u Kwankwaso ya yi farin jini.

Sai dai sun yi ta rera taken PDP tare da bayyana goyon bayansu ga dan takarar shugaban kasa na PDP Atiku Abubakar da dan takarar gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri.

Jagoran taron wanda tsohon sakataren jam’iyyar NNPP na shiyyar Arewa maso Gabas, Dr Babayo Liman ya ce sun fice daga NNPP ne saboda jam’iyyar na fama da rikici a jihohi da dama kuma shugaban na kasa wanda kuma ke neman zama shugaban kasa ya kasa magance su.

Babayo wanda dan jihar Bauchi ne, ya sanar da sauya sheka a farkon makon nan, inda ya ce magoya bayansa a Adamawa ne suka gayyace shi ya jagorance su zuwa PDP.

“Na sha samun gayyata daga jihohi daban-daban kuma da na zo nan (Adamawa), sai suka ce min suna son bin sawu na,” in ji shi, inda ya bayyana cewa akalla mutane 400,000 ne ke barin jam’iyyar NNPP zuwa PDP a jihar Adamawa.

Ya gabatar da wadanda suka biyo shi taron manema labarai da ya gudana a cibiyar ‘yan jarida ta NUJ da ke Yola, a matsayinsa na tsoffin jami’an NNPP na kananan hukumomin jihar Adamawa 21.

A yayin ganawar tasu da manema labarai, tsoffin ‘yan jam’iyyar NNPP sun cire kwankwasiyyarsu domin nuna alamar ficewarsu daga jam’iyyar NNPP.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp