Magoya bayan jam’iyyun adawa daban-daban na jihar Katsina sun shiga jam’iyyar APC mai mulki a ranar Lahadi.
Mafi yawan wadanda suka sauya sheka sun fito ne daga jam’iyyar PDP, New Nigeria Peoples Party (NNPP), Accord Party, PRP, da dai sauransu. Musamman ma, Rabiu Bakori, mataimakin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a zaben 2015 a Katsina yana cikin wadanda suka sauya sheka.
Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje, tare da mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa (NWC) ne suka tarbe su a hukumance a lokacin kaddamar da yakin neman zaben kananan hukumomi na jam’iyyar APC a karamar hukumar Ingawa.
Yayin da ya bayyana taron a matsayin mai tarihi, Ganduje ya tabbatar wa sabbin ‘ya’yan jam’iyyar cewa za su yi adalci, yana mai jaddada cewa jam’iyyar APC ce jam’iyyar da ta dukufa wajen ganin ta samar da ribar dimokuradiyya ta gaskiya. Ya ce, “Wadanda muke karba a yau sun fito ne daga jam’iyyun PDP, NNPP, Accord Party, APP, da PRP. An san Katsinawa da sadaukarwa, kwazon aiki, hadin kai, karbar baki, da kimar addini.”
Gwamnan jihar Katsina Dikko Radda shi ma ya bayyana kwarin guiwar ci gaba da samun nasarar jam’iyyar APC, inda ya yi alkawarin dorewar ayyukan ci gaban da aka fara a karkashin jam’iyyar. Ya kuma bai wa magoya bayansa tabbacin cewa jam’iyyar za ta yi nasara a zaben kananan hukumomin da aka shirya gudanarwa ranar 15 ga watan Fabrairun 2025.
“Muna maraba da masu sauya sheka sama da 100,000 a yau daga PDP, NNPP, PRP, da Accord Party, wadanda suka yarda da tasirin kokarinmu. Ga magoya bayanmu, ina kira gare ku da ku fito da yawan jama’a ku zabi jam’iyyar APC ba tare da tsoro ba. Ina tabbatar muku cewa za mu ci gaba da ayyukan alheri da muka faro a wannan gwamnati. Tsoffin gwamnoninmu, Sanatoci, da ‘yan Majalisar Wakilai sun ci gaba da kasancewa da hadin kai,” in ji Radda.