fidelitybank

Dubai ta sake tsaurara matakan bai wa ‘yan Najeriya biza

Date:

Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, UAE ta sake sanya wasu dokoki masu tsauri ga ‘yan Najeriya da ke neman bizar shiga ƙasarta domin yawon buɗe ido ko ziyarar wucin-gadi.

Sanarwar da ƙasar ta fitar ta haramta bai wa ‘yan Najeriya bizar wucin-gadi.

Sannan ɗuk wani ɗan Najeriya mai shekaru 18 zuwa 45 ba za a ba shi bizar shiga ƙasar ba, sai tafiyar ta kasance da iyali.

Wannan na zuwa ne kusan shekara ɗaya da UAE da Najeriya suka shawo kan matsalar haramcin bizar na shekara biyu da aka kakabawa ‘yan Najeriyar.

Amma dage haramcin ya zo da dokoki masu tsauri yanayin da ala tilas ya takaita wa ‘yan Najeriya shiga ƙasar.

Rahotanni na cewa a kullum batun samawa ‘yan Najeriyar bizar UAE na kara zama matsala cike da kalubale.

A yanzu dai wannan sabon doka na nufin an soke ba wa ‘yan Najeriya bizar wucin-gadi baki ɗaya

Sannan ga wanda ya haura shekara 45 idan yana neman biza sai ya gabatar da takardar bayanan asusun ajiyarsa na banki na tsawon wata shida, wanda zai nuna yana da kuɗaɗen da suka kai dala dubu 10 a lokacin neman bizar.

Sai kuma bukatar gabatar da Otel din da mutum zai yi masauki da kuma wasu bayanai na fasfo.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangote ya rage farashin litar mai zuwa ₦820

Kamfanin matatar man Dangote ya rage farashin litar mai...

Dubai ta sake tsaurara matakan bai wa ‘yan Najeriya biza

Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, UAE ta sake sanya wasu dokoki...

‘Yan Bindigar Katsina ‘yan asalin jihar mu ne – Gwamna

Gwamnan Katsina Umaru Dikko Radda ya ce galibin 'yan...

Zan yi wa ADC aiki ina cikin jam’iyyar PDP – Sule Lamido

Jigo a babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya...

Buhari da Tinubu kan su a hade ya ke – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari...

Ganduje ya kama aiki a hukumar kula da filayen jirgin sama

Tsohon shugaban jam'iyyar APC mai mulki, Abdullahi Ganduje, ya...

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...
X whatsapp