fidelitybank

DSS ta saki shugaban ƙungiyar ƙwadago bisa barazanar da ta yi na rufe ƙasar nan

Date:

Hukumar Tsaro ta farin kaya, DSS, ta saki Joe Ajaero, shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya.

An saki Ajaero da yammacin ranar Litinin da daddare kan belin gudanarwa a wani mataki da ake ganin a matsayin wani yunkuri na dakile yuwuwar rufe tattalin arzikin kasar.

Omoyele Sowore ya tabbatar da sakin Ajaero a wata sanarwa da ya fitar ta hanyar asusun sa na X a ranar Litinin da tsakar dare.

“BREAKING: Gwamnatin Fasist ta @officialABAT ta saki shugaban @NLCHeadquarters Joe Ajaero daga @OfficialDSSNG da ake tsare da shi kan belin,” ya rubuta akan X.com.

Sai dai NLC ba ta tabbatar da sakin sa a hukumance ba har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

Wannan na zuwa ne bayan NLC a cikin wata sanarwa ta yi barazanar rufe tattalin arzikin kasar idan ba a saki Ajaero ba kafin tsakar daren ranar Litinin.

DAILY POST ta tuna cewa an kama Ajaero da safiyar ranar Litinin a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, a lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa kasar Ingila domin ganawa a hukumance.

Kamen nasa dai ya jawo cece-kuce a ko’ina a fadin kasar inda kungiyoyin NLC da ‘yan kwadago suka yi kira da a gaggauta sakin sa.

Hakan na zuwa ne yayin da NLC ta umurci dukkanin kungiyoyin ta da su kasance cikin jajircewar daukar mataki idan ba a saki Ajaero ba.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp