fidelitybank

DSS ta gargaɗi NLC kan shiga yajin aiki

Date:

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS, ta yi kira ga ƙungiyar ƙwadago ta NLC da ta janye ƙudurinta na shirya zanga-zangar gama gari domin samun zaman lafiya a Najeriya.

NLC ta tsara shiga yajin aikin ranar 27 da 28 ga watan Fabarairu a wasu yankunan ƙasar domin nuna rashin jin daɗinta ga halin matsin rayuwa da ƴan Najeriya ke fuskanta da wasu matsaloli.

Wannan ya zo ne yayin da kwamishinan ƴan sanda a Abuja, CP Ben Igweh cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Josephine Adeh ta fitar, ya ce rundunarsa ba ta da masaniya kan zanga-zangar da ake shirin yi a Abuja.

Sanarwar ta DSS ɗauke da sa hannun Daraktan yaɗa labarai na hukumar, Dakta Peter Afunanya, ta ce DSS ta samu labarin akwai wasu mutane da ke shirin yin amfani da zanga-zangar wajen tayar da husuma da kuma rikici.

Sanarwar ta ce “an ankarar da mu game da shirin da ƙungiyar ƙwadago ke yi na gudanar da zanga-zanga. Yayin da hukumar ta ce haƙƙin ƴan ƙwadago ne su yi zanga-zanga sai dai ta yi kira ga ƙungiyar ta soke shirin domin zaman lafiyar al’umma.

“DSS ta kuma yi kira ga ƙungiyoyin su tattauna a maimakon yin abin da ka iya tayar da hankali. DSS ta ce ta samu bayanai cewa akwai wasu da ke son yin amfani da damar wajen janyo matsala da tashin hankali. Lamarin, ba tantama zai ƙara dagula yanayi da halin da ake ciki a sassan ƙasar.

“Abin da aka sani ne cewa gwamnati a matakai daban-daban tana ƙoƙarin warware matsalolin tattalin arziki a don haka, a ƙara ba su dama. Zuwa yanzu, hukumomin da suka dace na aiki ba dare ba rana tare da masu ruwa da tsaki domin bijiro da dabarun magance ƙalubalen da ake fuskanta. A don haka a basu dama su magance matsalolin da ake fuskanta.

DSS ta ce ya kamata masu son yin amfani da damar su sake tunani ganin cewa karkata ga irin waɗan nan munanan tunane-tunane ka iya kawo maƙarƙashiya ga zaman lafiya.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp