fidelitybank

DSS ta gargaɗi NLC kan shiga yajin aiki

Date:

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS, ta yi kira ga ƙungiyar ƙwadago ta NLC da ta janye ƙudurinta na shirya zanga-zangar gama gari domin samun zaman lafiya a Najeriya.

NLC ta tsara shiga yajin aikin ranar 27 da 28 ga watan Fabarairu a wasu yankunan ƙasar domin nuna rashin jin daɗinta ga halin matsin rayuwa da ƴan Najeriya ke fuskanta da wasu matsaloli.

Wannan ya zo ne yayin da kwamishinan ƴan sanda a Abuja, CP Ben Igweh cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Josephine Adeh ta fitar, ya ce rundunarsa ba ta da masaniya kan zanga-zangar da ake shirin yi a Abuja.

Sanarwar ta DSS ɗauke da sa hannun Daraktan yaɗa labarai na hukumar, Dakta Peter Afunanya, ta ce DSS ta samu labarin akwai wasu mutane da ke shirin yin amfani da zanga-zangar wajen tayar da husuma da kuma rikici.

Sanarwar ta ce “an ankarar da mu game da shirin da ƙungiyar ƙwadago ke yi na gudanar da zanga-zanga. Yayin da hukumar ta ce haƙƙin ƴan ƙwadago ne su yi zanga-zanga sai dai ta yi kira ga ƙungiyar ta soke shirin domin zaman lafiyar al’umma.

“DSS ta kuma yi kira ga ƙungiyoyin su tattauna a maimakon yin abin da ka iya tayar da hankali. DSS ta ce ta samu bayanai cewa akwai wasu da ke son yin amfani da damar wajen janyo matsala da tashin hankali. Lamarin, ba tantama zai ƙara dagula yanayi da halin da ake ciki a sassan ƙasar.

“Abin da aka sani ne cewa gwamnati a matakai daban-daban tana ƙoƙarin warware matsalolin tattalin arziki a don haka, a ƙara ba su dama. Zuwa yanzu, hukumomin da suka dace na aiki ba dare ba rana tare da masu ruwa da tsaki domin bijiro da dabarun magance ƙalubalen da ake fuskanta. A don haka a basu dama su magance matsalolin da ake fuskanta.

DSS ta ce ya kamata masu son yin amfani da damar su sake tunani ganin cewa karkata ga irin waɗan nan munanan tunane-tunane ka iya kawo maƙarƙashiya ga zaman lafiya.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp