Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta bankado wani shiri na haddasa rikici a sassan kasar nan, musamman a yankin Arewa ta tsakiya.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar DSS, Peter Afunanya, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Abuja.
Sai dai ya ce an dauki matakan dakile wannan shiri na wasu marasa kishin al’umma.
“Yayin da ke kallon makircin a matsayin rashin kishin kasa, tana kan hanyar jami’an tada zaune tsaye wadanda ke da sha’awar yin amfani da tashin hankali don cimma munanan manufofin.
“Duk da cewa ta sanya matakan kawo cikas ga wadannan dabi’un, ta na gargadin shugabannin da ‘yan kungiyarsu da su kaurace wa ayyukan da za su iya haifar da karya doka da oda,” in ji shi.
Afunanya ya ce an shirya shirin ne domin haifar da rikicin kabilanci da addini, da tayar da kayar baya da kuma zafafa harkokin siyasa.
A cewarsa, a kokarin ganin an cimma hakan, wadanda suka dauki nauyin haka, sun tara mutanen su tare da gudanar da tarurruka da dama a ciki da wajen wuraren da za a kai harin.
Ya ce hukumar ta na sane da wani shiri na yin amfani da dalibai, malaman jami’o’i da ke yajin aiki, kungiyoyin kwadago, marasa galihu da kuma wasu kungiyoyi domin haddasa rikicin.
A cewar Afunanya, manufar kuma ita ce a yi amfani don gudanar da zanga-zangar gama gari kamar # ENDSARS, duk da kokarin da gwamnati ke yi na magance matsalolin.