fidelitybank

DSS ta bankaɗo wani shirin haddasa rikici da ake kokarin yi a yankin Arewa ta tsakiya

Date:

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta bankado wani shiri na haddasa rikici a sassan kasar nan, musamman a yankin Arewa ta tsakiya.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar DSS, Peter Afunanya, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Abuja.

Sai dai ya ce an dauki matakan dakile wannan shiri na wasu marasa kishin al’umma.

“Yayin da ke kallon makircin a matsayin rashin kishin kasa, tana kan hanyar jami’an tada zaune tsaye wadanda ke da sha’awar yin amfani da tashin hankali don cimma munanan manufofin.

“Duk da cewa ta sanya matakan kawo cikas ga wadannan dabi’un, ta na gargadin shugabannin da ‘yan kungiyarsu da su kaurace wa ayyukan da za su iya haifar da karya doka da oda,” in ji shi.

Afunanya ya ce an shirya shirin ne domin haifar da rikicin kabilanci da addini, da tayar da kayar baya da kuma zafafa harkokin siyasa.

A cewarsa, a kokarin ganin an cimma hakan, wadanda suka dauki nauyin haka, sun tara mutanen su tare da gudanar da tarurruka da dama a ciki da wajen wuraren da za a kai harin.

Ya ce hukumar ta na sane da wani shiri na yin amfani da dalibai, malaman jami’o’i da ke yajin aiki, kungiyoyin kwadago, marasa galihu da kuma wasu kungiyoyi domin haddasa rikicin.

A cewar Afunanya, manufar kuma ita ce a yi amfani don gudanar da zanga-zangar gama gari kamar # ENDSARS, duk da kokarin da gwamnati ke yi na magance matsalolin.

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp