Jami’an tsaro na farin kaya, DSS sun kama wani da ake zargi da siyan kuri’u a zaben gwamnan jihar Ondo da ke gudana.
An kama wanda ake zargi da siyan kuri’u da buhu biyu na kudi da ake kyautata zaton an yi shi ne domin jawo hankalin masu kada kuri’a.
An kama shi ne a Ward 4, Polling Unit 007 a wajen makarantar St. Stephen’s Primary School, Akure, Jihar Ondo, da misalin karfe 9:00 na safe a ranar zabe.
A halin da ake ciki, Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya kada kuri’arsa a rumfar zabe mai lamba 6, Ward 4 a Obenla, karamar hukumar Ilaje.
Aiyedatiwa dai ya fafata ne domin ya ci gaba da rike kujerar gwamna a zaben fitar da gwani da wasu ‘yan takara 16 daga jam’iyyu daban-daban ciki har da Agboola Ajayi na jam’iyyar PDP.