fidelitybank

DSS sun kama Basarake bayan an tsigewa DPO kai

Date:

Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta DSS, sun cafke Sarkin masarautar Akoh na jihar Ribas, mai martaba Eze Ikegbidi.

Kamen wanda aka gudanar a ranar Litinin din da ta gabata ya biyo bayan wani mummunan kisan gilla da wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan kungiyar ne suka yi wa jami’in ‘yan sanda reshen Ahoada, Bako Angbashim.

A daren Juma’a ne maharan suka kashe DPO tare da fille masa kai a wani samame tare da mutanensa a yankin.

Kame Ikegbidi da jami’an DSS suka yi ya biyo bayan dakatarwar da gwamnan jihar, Siminilayi Fubara ya yi masa na tsawon lokaci.

Gwamna Fubara a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya zargi sarkin da “bawa shahararren David Gift wanda aka fi sani da 2-Baba da ‘yan kungiyarsa su gudanar da ayyukansu cikin walwala.

Gwamnan ya kuma bayar da ladar Naira miliyan 100,000,000 ga babban wanda ake tuhuma, inda ya ce duk wanda ke da bayanai masu amfani da za su kai ga kama shi da kuma gurfanar da shi a gaban kuliya to ya kai rahoto ga hukumomin da abin ya shafa.

An tattaro cewa daga baya an mika sarkin ga hukumar leken asiri da binciken manyan laifuka ta jihar dake Fatakwal, babban birnin jihar domin yi masa tambayoyi.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ribas, DSP Grace Iringe-Koko, ta ce ba ta da cikakken bayani kan kamun.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp