fidelitybank

DSS na shirin sake kama Emefiele – Lauya

Date:

Lauyoyin tsohon gwamnan babban bankin Najeriya da aka dakatar, Godwin Emefiele, sun koka kan yadda ma’aikatan gwamnatin tarayya ke shirin sake kama wanda suke karewa duk da belin da wata babbar kotun tarayya da ke Legas ta ba shi.

A cewar gidan talabijin na Channels, babban lauyan Najeriya (SAN), Joseph Daudu, ya bayyana hakan jim kadan bayan zaman kotun a Legas.

Kotu ce ta bayar da belin Emefiele kan kudi Naira miliyan 20 bayan gurfanar da shi gaban kuliya bisa zargin mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

Daudu ya yi zargin cewa a halin yanzu hukumar ta DSS ta daura damarar sake kama Emefiele duk da hukuncin.

Har ya zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, har yanzu gwamnan CBN da aka dakatar yana can a cikin dakin shari’a tare da lauyoyinsa.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp