fidelitybank

Dole sai Emefiele ya sauka daga mukaminsa kafin tsayawa takarfa – Kotu

Date:

Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ta ki yarda da bukatar Gwamnan Babban Bankin kasa na (CBN), Godwin Emiefele ta ba shi kariyar neman takarar shugaban kasa ba tare da ya sauka daga kujerarsa ba.

Mista Emiefele dai ya gabatar da bukatar kotun ta ayyana cewa, yana da damar neman takarar shugabancin a karkashin duk jam’iyyar da yake so, yayin da yake rike da mukamin gwamnan bankin.

Tun da farko a yau Litinin lauyan Emiefele, Mike Ozekhome, ya bukaci kotun da ta amsa bukatarsu ta bayar da umarni na wucin-gadi na hana Hukumar Zabe ta Najeriya (INEC) da Babban Lauyan gwamnati kuma Ministan Shari’a na Tarayya daga hana shi shiga zaben fitar da gwani na duk jam’iyyar da yake so.

Da yake zartar da hukunci, alkalin kotun Ahmed Mohammed, ya ayyana cewa, maimakon haka sai dai ya umarci hukumar zaben da Babban Lauyan su bayyana a gabanta ranar 12 ga watan Mayu domin su bayar da bahasinsu kan dalilin da suke ganin kotun bai kamata ta amsa bukatar Mista Emiefele ba.

A zaman na yau Litinin, lauyan gwamnan ya ce zuwa ranar Laraba 11 ga watan Mayu, wa’adin karbar takardar bayyana sha’awar yin takarar shugaban kasar zai kare

A ainahin karar da lauyan Gwamnan Babban Bankin ya gabatar ranar biyar ga watan Mayu, 2022, lauyan ya ce babu wata dokar kasar da ta hana Mista Emiefele takara yana rike da kujerar shugabancin bankin.

Ana matsa wa Mista Emefiele lamba ne da ya sauka daga mukami tun bayan da bayanai suka bayyana na aniyarsa ta neman takarar shugabancin kasar a jam’iyya mai mulkin kasar, APC, a farkon shekarar nan.

A watan Fabrairu na shekara mai zuwa ne 2023, za a yi babban zaben kasa a Najeriya, inda za a zabi wanda zai gaji Shugaba Muhammdu Buhari wanda zai kammala wa’adinsa na biyu na shekara hudu-hudu.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla ÆŠanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An É—age jana’izar Aminu ÆŠantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da É—age jana'izar fitaccen É—ankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp