Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ta ki yarda da bukatar Gwamnan Babban Bankin kasa na (CBN), Godwin Emiefele ta ba shi kariyar neman takarar shugaban kasa ba tare da ya sauka daga kujerarsa ba.
Mista Emiefele dai ya gabatar da bukatar kotun ta ayyana cewa, yana da damar neman takarar shugabancin a karkashin duk jam’iyyar da yake so, yayin da yake rike da mukamin gwamnan bankin.
Tun da farko a yau Litinin lauyan Emiefele, Mike Ozekhome, ya bukaci kotun da ta amsa bukatarsu ta bayar da umarni na wucin-gadi na hana Hukumar Zabe ta Najeriya (INEC) da Babban Lauyan gwamnati kuma Ministan Shari’a na Tarayya daga hana shi shiga zaben fitar da gwani na duk jam’iyyar da yake so.
Da yake zartar da hukunci, alkalin kotun Ahmed Mohammed, ya ayyana cewa, maimakon haka sai dai ya umarci hukumar zaben da Babban Lauyan su bayyana a gabanta ranar 12 ga watan Mayu domin su bayar da bahasinsu kan dalilin da suke ganin kotun bai kamata ta amsa bukatar Mista Emiefele ba.
A zaman na yau Litinin, lauyan gwamnan ya ce zuwa ranar Laraba 11 ga watan Mayu, wa’adin karbar takardar bayyana sha’awar yin takarar shugaban kasar zai kare
A ainahin karar da lauyan Gwamnan Babban Bankin ya gabatar ranar biyar ga watan Mayu, 2022, lauyan ya ce babu wata dokar kasar da ta hana Mista Emiefele takara yana rike da kujerar shugabancin bankin.
Ana matsa wa Mista Emefiele lamba ne da ya sauka daga mukami tun bayan da bayanai suka bayyana na aniyarsa ta neman takarar shugabancin kasar a jam’iyya mai mulkin kasar, APC, a farkon shekarar nan.
A watan Fabrairu na shekara mai zuwa ne 2023, za a yi babban zaben kasa a Najeriya, inda za a zabi wanda zai gaji Shugaba Muhammdu Buhari wanda zai kammala wa’adinsa na biyu na shekara hudu-hudu.