Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya yi alkawarin cewa, za a sa lalle ilalla Rasha ta biya kudin ɓarnar da take yi a kasarsa.
A wani sako da ya aike ta hoton bidiyo Shugaban ya lashi takobin cewa za a gyara duk wani gida da titi da aka lalata a Ukraine.
A halin da ake ciki dai Rashar ta ci gaba da kai hare-haren mamayar da take yi wa kasar, makwabciyarta.
Birnin Mariupol mai tasahar jirgin ruwa, wanda ke da matukar muhimmanci na ci gaba da shan ruwan makamai masu linzami, daga dakarun Rasha da suka yi masa kawanya.
Mataimakin magajin garin birnin (Sergei Orlov) ya gaya wa BBC cewa, an katse wa mutanen birnin wutar lantarki, da naurarar dumama gida da kuma ruwa.
Ya ce halin da jama’a ke ciki ya munana, “an aci gaba da harba makamai da ruwan bamabamai, yanayin da ake ciki na farar hula, a iya cewa muna cikin mawuyacin hali.”
Mista Orlov ya kuma ce, abu ne mai wuyar gaske a iya kwaso dukkanin gawarwakin mutnen da aka kashe, kuma ya yi kiyasin cewa sama da farar hula 200 aka kashe ko jikkata.