fidelitybank

Dole ne sai an biya ‘yan Fansho kafin a biya ma’aikatan gwamnati – Otti

Date:

Gwamnan jihar Abia, Alex Otti ya bayar da umarnin cewa dole ne ma’aikatan gwamnati da masu karbar fansho a jihar Abia su karbi albashinsu kafin a biya masu rike da mukaman siyasa albashi.

Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ya koka kan yadda gwamnatocin da suka gabata a jihar suka dade suna bin ‘yan fansho, kafin daga bisani gwamnatinsa ta wanke kudaden fansho da ba a biya ba.

Gwamna Otti ya bayyana haka ne a sakonsa na Easter ga ‘yan asalin jihar Abia, yana mamakin dalilin da ya sa aka hana ma’aikatan gwamnati da suka yi wa jihar hidima na tsawon lokaci mai tsawo.

Ya yi nuni da cewar bai kamata biyan mutane kudaden fansho ya zama abin burgewa ba amma ya bayyana cewa farin cikin da ke cikin fuskokin wadanda suka yi ritaya ya samo asali ne daga basussukan da ake bin su na tsawon lokaci.

“Hakika abin takaici ne a ce wadannan manya maza da mata (’yan fansho), wadanda suka yi wa kasa aiki a kololuwar shekarun da suka yi na samun ci gaba, an dade ana bin su.

“Ko ta yaya, kamar yadda na ambata a cikin jawabina ga Abians jim kadan bayan rantsar da ni, ba za a sake fuskantar manyan ‘yan kasarmu da azabar rashin biyansu hakkokinsu ba.

“Tun daga nan na ba da umarnin a biya cikakken kudaden fansho ko kafin ranar 28 ga wata, a ranar ne ma’aikatan gwamnati ke samun albashin su.

“A bisa ka’ida, masu rike da mukaman siyasa za a biya su ne kawai bayan an cika nauyin da ya rataya a wuyanmu ga manya da ma’aikatan gwamnati, gaba daya,” in ji Gwamna Otti.

Ya godewa shuwagabannin kungiyar da ‘yan kungiyar ’yan fansho ta Najeriya a jihar kan yadda suka amince da gwamnatinsa, inda ya jaddada cewa jin dadin al’ummar Abia na da matukar muhimmanci ga gwamnatinsa.

Ya bayyana cewa Abia ta zama daya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a kasar nan kuma ya shawarci ‘yan asalin Abia da masu ziyara da su zagaya da saka hannun jari a jihar ba tare da tsoro ba.

Ya taya al’ummar Abia da Kirista baki daya murnar bikin Ista na bana, yana mai cewa babu wani yanki na jihar da za a bar shi ba tare da ci gaban sa ba.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp