fidelitybank

Dole ne Najeriya ta ɗaure a kan manufofin ta na farfaɗo da tattalin arziki – Bankin Duniya

Date:

Bankin Duniya ya ce dole ne Najeriya ta ci gaba da yin tsare-tsaren da take kai a yanzu na tsawon aƙalla shekara 15, muddin tana son ɗorewar tattalin arzikinta.

Mataimaikin shugaban bankin, Mr Indermit Gill ne ya bayyana haka a wani taron tattalin arziki karo na 30 da aka yi a Abuja ranar Litinin.

Ya ce ya kamata gwamnati ta jajirce wajen ci gaba da tsare-tsarenta na yanzu domin shawo kan matsaloli da ƙasar ke fuskanta wanda kuma suka janyo rashin cigaba tsawon lokaci.

“Babu wani wayo da za a yi a batun gyaran tattalin arziki. Ya kamata Najeriya ta tsaya kan tsare-tsarenta na tsawon shekara 15. Tsare-tsaren da aka ɗauka yanzu ba za su yi daɗi ba ko kuma kawo sakamako mai kyau nan take, amma za su ɗora ƙasar kan turbar cigaba mai ɗorewa,” in ji shi.

Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin ƴan Najeriya ke ci gaba da nuna fushinsu kan cire tallafin man fetur da gwamnati ta yi da kuma tashin farashin dala.

Duk da cewa waɗannan tsare-tsare sun janyo tsadar rayuwa da kuma wahalhalu daban-daban ga ƴan ƙasar, jami’in na Bankin Duniya ya ce komawa baya ba zai haifar da ɗa mai ido ga tattalin arzikin ƙasar ba.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp