fidelitybank

Dole ne mu tsaya a biwa mutanen Tudun Biri hakkin su – Sarkin Musulmi

Date:

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya ce kungiyar da yake jagorantar Jama’atu Nasril Islam, za ta nemi a tabbatar da adalci ga mutanen da harin jirgin sojojin Najeriya maras matuki ya aukawa bisa kuskure a cikin jihar Kaduna.

Sarkin Musulmi ya ba da wannan tabbaci ne yayin babban taron kungiyar Jama’atu Nasril Islam na shekara-shekara a ranar Litinin din nan, daidai lokacin da gwamnatin Najeriya ta sake neman afuwa a kan abin da ya faru, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

“A matsayinmu na cikakkun Musulmai, mun dauka cewa abin da ya faru kaddara ce daga Allah kuma za mu duba, mu ga abin da za mu iya yi ga wadanda wannan harin ya shafa, za mu tabbatar da mun yi ta bibiya don ganin an yi adalci.

“Ba ma ganin kowa amma muna son ganin an yi wa kowa adalci. A matsayinmu na Musulmai dukkanmu mun ji takaici kan abin da ya faru,” a cewarsa.

Game da taron na Jama’atu Nasril Islam, Sarkin Musulmi ya ce an tsara shi ne don tattaunawa kan batutuwan da ke faruwa a fadin duniya game da Musulmai da kuma addinin Musulunci.

Ya yi kira ga gwamnatin Najeriya ta mayar da hankali wajen gyaran titunan kasar musamman titin Minna zuwa Suleja da Minna zuwa Bida wadanda ke cikin mummunan yanayi a jihar Neja.

A jawabinsa, ministan yada labarai na Najeriya, Alhaji Mohammed Idris ya sake nanata neman afuwar Shugaba Bola Tinubu da kuma jajantawa kan mummunan harin jirgin sama maras matuki da ya yi sanadin mutuwar gomman mutane da jikkata wasu da dama a garin Tudun Biri.

Ya ce shugaban kasar ya amince da fara shirin FULAKO, wanda zai ba da damar gina gidaje da kananan asibitoci da makarantu da dakunan kula da lafiyar dabbobi a wani bangare na bin matakan da ba na soji ba, ga rikice-rikicen ‘yan fashin daji da na satar mutane don kudin fansa a arewa.

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp