fidelitybank

Dole ne mu tsaya a biwa mutanen Tudun Biri hakkin su – Sarkin Musulmi

Date:

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya ce kungiyar da yake jagorantar Jama’atu Nasril Islam, za ta nemi a tabbatar da adalci ga mutanen da harin jirgin sojojin Najeriya maras matuki ya aukawa bisa kuskure a cikin jihar Kaduna.

Sarkin Musulmi ya ba da wannan tabbaci ne yayin babban taron kungiyar Jama’atu Nasril Islam na shekara-shekara a ranar Litinin din nan, daidai lokacin da gwamnatin Najeriya ta sake neman afuwa a kan abin da ya faru, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

“A matsayinmu na cikakkun Musulmai, mun dauka cewa abin da ya faru kaddara ce daga Allah kuma za mu duba, mu ga abin da za mu iya yi ga wadanda wannan harin ya shafa, za mu tabbatar da mun yi ta bibiya don ganin an yi adalci.

“Ba ma ganin kowa amma muna son ganin an yi wa kowa adalci. A matsayinmu na Musulmai dukkanmu mun ji takaici kan abin da ya faru,” a cewarsa.

Game da taron na Jama’atu Nasril Islam, Sarkin Musulmi ya ce an tsara shi ne don tattaunawa kan batutuwan da ke faruwa a fadin duniya game da Musulmai da kuma addinin Musulunci.

Ya yi kira ga gwamnatin Najeriya ta mayar da hankali wajen gyaran titunan kasar musamman titin Minna zuwa Suleja da Minna zuwa Bida wadanda ke cikin mummunan yanayi a jihar Neja.

A jawabinsa, ministan yada labarai na Najeriya, Alhaji Mohammed Idris ya sake nanata neman afuwar Shugaba Bola Tinubu da kuma jajantawa kan mummunan harin jirgin sama maras matuki da ya yi sanadin mutuwar gomman mutane da jikkata wasu da dama a garin Tudun Biri.

Ya ce shugaban kasar ya amince da fara shirin FULAKO, wanda zai ba da damar gina gidaje da kananan asibitoci da makarantu da dakunan kula da lafiyar dabbobi a wani bangare na bin matakan da ba na soji ba, ga rikice-rikicen ‘yan fashin daji da na satar mutane don kudin fansa a arewa.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp