Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman, ya gargadi malaman jami’o’i kan cin zarafi da ake yi a harabar jami’o’in, yana mai jaddada cewa ma’aikatar za ta yi taka-tsan-tsan da masu aikata irin wadannan ayyuka.
Mamman ya yi wannan gargadin ne a Abuja ranar Alhamis a lokacin da ya karbi rahoton kwamitin kan cin zarafin da shugaban tsangayar shari’a na Jami’ar Calabar, Farfesa Cyril Ndifo ya yi.
Ya ce cin zarafi na fyaɗe babban laifi ne wanda dole ne a yi hukunci mai tsauri a duk lokacin da ya faru.
A cewarsa, ma’aikatar za ta yi duk mai yiwuwa na dan Adam wajen dakile munanan tashe-tashen hankula a cibiyoyin ilimi.