fidelitybank

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Date:

Tsagin tsohuwar jam’iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP da ke cikin babbar jam’iyyar APC da ke mulki a Najeriya sun ce lallai ne a bar musu kujerar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027, inda suka buƙaci shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya yi watsi da buƙatar nemo wani daban.

Tsagin ANPP ɗin sun ce su ne na biyu wajen ƙarfi a haɗakar da aka yi a shekarar 2013 da ta haifar da jam’iyyar APC, inda suka yi barazanar cewa yin watsi da su a tikitin takarar zaɓen 2027 zai iya tilasta musu su fara tunanin sauya sheka daga APC, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Ƙungiyar tsofaffin mambobin ANPP ne suka bayyana haka a wani taron manema labarai a ranar Litinin a Abuja, inda suka ce ba a saka musu yadda ya dace ba bisa babbar gudunmuwar da suka bayar wajen kafa jam’iyyar APC.

Jagoran ƙungiyar Farfesa Vitalis Orikeze Ajumbe ya ce, “za a samu matsala a takarar 2027 idan aka ɗauki wanda ba ɗan tsagin ANPP ba a matsayin mataimakin shugaban ƙasa.”

Ya ce tsaginsu na ANPP ya sha wahala tare da fuskantar wariya a zamanin mulkin Marigayi Muhammadu Buhari.

Ya ce daga cikin mambobin su akwai mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima da gwamnoni irin su Babagana Umara Zulum na jihar Borno da Mai Mala Buni na jihar Borno da tsofaffin gwamnoni irin su Attahiru Bafarawa da Sani Yarima Bakura da Ali Modu Sheriff da sauran su.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp