fidelitybank

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Date:

Tsagin tsohuwar jam’iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP da ke cikin babbar jam’iyyar APC da ke mulki a Najeriya sun ce lallai ne a bar musu kujerar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027, inda suka buƙaci shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya yi watsi da buƙatar nemo wani daban.

Tsagin ANPP ɗin sun ce su ne na biyu wajen ƙarfi a haɗakar da aka yi a shekarar 2013 da ta haifar da jam’iyyar APC, inda suka yi barazanar cewa yin watsi da su a tikitin takarar zaɓen 2027 zai iya tilasta musu su fara tunanin sauya sheka daga APC, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Ƙungiyar tsofaffin mambobin ANPP ne suka bayyana haka a wani taron manema labarai a ranar Litinin a Abuja, inda suka ce ba a saka musu yadda ya dace ba bisa babbar gudunmuwar da suka bayar wajen kafa jam’iyyar APC.

Jagoran ƙungiyar Farfesa Vitalis Orikeze Ajumbe ya ce, “za a samu matsala a takarar 2027 idan aka ɗauki wanda ba ɗan tsagin ANPP ba a matsayin mataimakin shugaban ƙasa.”

Ya ce tsaginsu na ANPP ya sha wahala tare da fuskantar wariya a zamanin mulkin Marigayi Muhammadu Buhari.

Ya ce daga cikin mambobin su akwai mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima da gwamnoni irin su Babagana Umara Zulum na jihar Borno da Mai Mala Buni na jihar Borno da tsofaffin gwamnoni irin su Attahiru Bafarawa da Sani Yarima Bakura da Ali Modu Sheriff da sauran su.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp