fidelitybank

Dole ne a zakulo wanda suka kashe mana jami’ai 17 – Sojoji

Date:

Rundunar sojojin ƙasa ta ce, dakarunta ba za su fice daga jihar Delta ba har sai an zaƙulo waɗanda suka kashe sojoji 17 a baya-bayan nan.

Kwamandan runduna ta shida da ke aiki ƙarƙashin rundunar ko ta kwana a yankin kudu maso kudancin Najeriya, Manjo Janar Jamal Abdussalam ya bai wa shugabannin yankin Neja Delta tabbacin cewa sojoji za su nuna ƙwarewa wajen nemo mutanen da ke da hannu a kisan gillar da aka yi wa sojojin.

Ya bayyana haka ne lokacin da shugaban hukumar raya yankin Neja Delta Chif Samuel Ogbuku ya kai masa ziyara a hedikwatar rundunar da ke barikin sojoji a Patakwal.

Rundunar sojin cikin sanarwar da ta fitar ranar Alhamis ta ruwaito manjo janar Abdussalam na cewa nauyin da aka ɗora wa sojojin shi ne su gano makaman da ɓata-garin suka ƙwace daga hannun sojojin da aka kashe tare da tabbatar da cewa an kama duka masu hannu a kisan gillar.

Ya ƙara da cewa sojoji za su ci gaba da kasancewa a jihar har sai an cimma ƙudurin da aka sa gaba na binciko waɗanda suka tafka aika-aikar.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp