Gwamnatin jihar Jigawa ta ce, dole ne a yi adalci tare da hukunta wadanda aka samu da hannu akan fashewar iskar gas da ta shafa a jihar kwanan nan.
Mataimakin gwamnan jihar Malam Umar Namadi ya bada wannan tabbacin lokacin da ya ziyarci Hakimin Babura Sarkin ban Ringim Nata`ala Mustapha a fadar sa.
Motar da ake zargin tana dauke ne da bututun iskar gas ta fashe a yayin da jami’an kwastam suka bi ta kan iyakar kasar.
Mutane 6 ne suka jikkata, kana shaguna goma sha bakwai da gidaje biyu sun lalace a lamarin.
Mataimakin Gwamnan yayin da yake jajantawa wadanda lamarin ya rutsa da su ya ce, gwamnatin jihar ta damu matuka da faruwar lamarin kuma ta dukufa wajen shawo kan lamarin.