Matar nan da shugaba Bola Tinubu ya cire sunanta daga cikin jerin sunayen da ya aike wa majalisar datawa don tantance su a matsayin ministocin gwamnatinsa Dakta Maryam Shetty ta ce, ƙaddara ce ta sa a ka cire sunanta.
Cikin wani dogon saƙo da ta wallafa a shafiunta na Facebook Maryam Shetty ta ce ba za ta iya bayyana irin farin cikin da ta ji ba a lokacin da ta ga sunanta cikin jerin mutanen da ake son nadawa a matsayin ministocin kasar.
Kuma hakan a cewarta wata alama ce da ke nuna cewa a shirye Najeriya take wajen tabbatar da kyakkyawar makomar mata musamman matasa a kamarta.
To sai dai Dakta shetty ta ce ƙaddara wadda ta riga fata ta yi tasiri wajen cire sunanta daga jerin sunayen.
Ta ce ”wasu na ganin hakan tamkar wani koma-baya ne a gareni, amma ni a matsayina na musulma na yadda da ƙaddara, na ɗauki hakan a matsayin ƙaddara daga Allah, wanda shi ke bayar da mulki ga wanda ya so, kuma a lokacin da ya so”.
Ta kuma ƙara da cewa duk, da wannan abin da ya faru, tana miƙa godiyarta ga shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu kan sanya sunanta da ya yi tun da farko.
Dakta Maryam ta kuma ce hakan bai karya mata gwiwa ba, domin kuwa a cewarta tana cike da ƙwarin gwiwar bauta wa ƙasarta.
”Ina son tabbatar wa magoya baya na cewa wannan ba shi ne ƙarshe ba, yanzu ma aka fara, don haka ku ci gaba da yi wa ƙaramu addu’a tare da goya wa shugaban ƙasarmu baya”.
A ranar Laraba ne shugaban ƙasar ya aike da sunayen mutum 19 ciki har da Dakta Maryam Shetti ga Majalisar Dattawan kasar domin tantance su a matsayin ministoci.
Sanya sunan Shetty cikin jerin sunayen ya janyo zazzafar muhawara musamman a shafukan sada zumunta a arewacin ƙasar, kasancewar sunan nata ya zo wa mutane da dama da mamaki.
To sai dai kuma a ranar Juma’a ana tsaka da tantance ministocin, sai shugaban kasar ya sake aika sunan mutum biyu zuwa majalisar, inda a ciki ya bayyana janye sunan Dakta Maryam Shetty, inda ya maye gurbinta da Dakta Mariya Mairiga Mahmud.