fidelitybank

Dole ne a yaba wa Tinubu – Maryam Shetty

Date:

Matar nan da shugaba Bola Tinubu ya cire sunanta daga cikin jerin sunayen da ya aike wa majalisar datawa don tantance su a matsayin ministocin gwamnatinsa Dakta Maryam Shetty ta ce, ƙaddara ce ta sa a ka cire sunanta.

Cikin wani dogon saƙo da ta wallafa a shafiunta na Facebook Maryam Shetty ta ce ba za ta iya bayyana irin farin cikin da ta ji ba a lokacin da ta ga sunanta cikin jerin mutanen da ake son nadawa a matsayin ministocin kasar.

Kuma hakan a cewarta wata alama ce da ke nuna cewa a shirye Najeriya take wajen tabbatar da kyakkyawar makomar mata musamman matasa a kamarta.

To sai dai Dakta shetty ta ce ƙaddara wadda ta riga fata ta yi tasiri wajen cire sunanta daga jerin sunayen.

Ta ce ”wasu na ganin hakan tamkar wani koma-baya ne a gareni, amma ni a matsayina na musulma na yadda da ƙaddara, na ɗauki hakan a matsayin ƙaddara daga Allah, wanda shi ke bayar da mulki ga wanda ya so, kuma a lokacin da ya so”.

Ta kuma ƙara da cewa duk, da wannan abin da ya faru, tana miƙa godiyarta ga shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu kan sanya sunanta da ya yi tun da farko.

Dakta Maryam ta kuma ce hakan bai karya mata gwiwa ba, domin kuwa a cewarta tana cike da ƙwarin gwiwar bauta wa ƙasarta.

”Ina son tabbatar wa magoya baya na cewa wannan ba shi ne ƙarshe ba, yanzu ma aka fara, don haka ku ci gaba da yi wa ƙaramu addu’a tare da goya wa shugaban ƙasarmu baya”.

A ranar Laraba ne shugaban ƙasar ya aike da sunayen mutum 19 ciki har da Dakta Maryam Shetti ga Majalisar Dattawan kasar domin tantance su a matsayin ministoci.

Sanya sunan Shetty cikin jerin sunayen ya janyo zazzafar muhawara musamman a shafukan sada zumunta a arewacin ƙasar, kasancewar sunan nata ya zo wa mutane da dama da mamaki.

To sai dai kuma a ranar Juma’a ana tsaka da tantance ministocin, sai shugaban kasar ya sake aika sunan mutum biyu zuwa majalisar, inda a ciki ya bayyana janye sunan Dakta Maryam Shetty, inda ya maye gurbinta da Dakta Mariya Mairiga Mahmud.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp