Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya wajabta karanta alkawarin biyayya ga Najeriya a duk tarukan gwamnati da na jama’a a kasar.
Kakakin shugaban kasar Ajuri Ngelale ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa ranar Alhamis inda ya ce yin hakan nuna girmamawa ne ga kasa da kuma karfafa biyayya ga dokokin kasa tare da alkinta al’adu da martaba kasa.
Shugaban ya jaddada bukatar yin biyayya ga manufofin kasa da nuna kima ga dokokin kasa.
Taken na yi wa Najeriya alkawarin biyayya wanda Tinubu ya ce a yi bayan rera taken kasa, na neman yan kasa su zama masu gaskiya da biyayya ga kasarsu.
Umarnin ya zo ne daidai lokacin da Najeriya ke fama da rikice-rikice da tashin hankali tsakanin arewaci da kudancin kasar.