Firaiministan Spain Pedro Sanchez ya ce, a shirye suke su amince da fara ɗaukar Falasɗinu a matsayin ƙasa inda wanda wannan mataki zai share hanyar kawo matsalar da Gabas ta Tsakiya ke ciki.
Lokacin da yake bayani ga majalisar Spain yau da safe, ya ce wannan wani muradi ne da ya fito daga nahiyar Turai da kuma shugabannin EU da ke nuna goyon bayan amincewar.
Ya kuma harin ramuwar gayyar da Isra’ila ke kai wa da aka kai mata a watan Oktoba ya wuce iyaka.
Sanchez yana cikin masu fitowa ƙarara su soki Isra’ila tun lokacin da ta fara ƙaddamar da harin soji na ramuwa. In ji BBC.